Gwamna Ya Yi Jirwaye Mai Kama da Wanka kan Shiga APC, Ya Fadi Shirin da Suke Yi
- Gwamna Bala Mohammed ya magantu kan rade-radin komawa APC, yana cewa zai ci gaba da zama a PDP duk da matsalolin da ke cikinta
- Ya ce siyasa na iya sauyawa, amma za su dauki matakai cikin hikima da dabara ba tare da yin kuskure ba
- Gwamnan ya yi alkawarin biyan albashi kan lokaci da kuma warware basussukan giratuti kafin ya kammala wa’adin mulkinsa
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Bauchi - Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya yi karin haske yayin da ake ta yada cewa zai koma APC a Najeriya.
Wannan jita-jita na zuwa ne bayan kusan dukan gwamnonin PDP a Najeriya sun sauya sheka zuwa APC mai mulkin Najeriya.

Source: Twitter
Legit Hausa ta samu wannan bayani ne daga shafin @emmaikumeh wanda ya wallafa bidiyon a shafinsa na X.
Gwamna Bala ya magantu kan rade-radin komawa APC
Gwamna Bala ya tabbatar da cewa akwai matsaloli a PDP kamar yadda kowa ya sani amma dai ita siyasa komai na iya faruwa.
Ya tabbatar da cewa ba zai je ko ina ba duk da tarun matsalolin da ke cikin PDP inda ya ce za su iya kasancewa a ko ina amma dai cikin dabara ba za su bari kansu ya yi murfi ba.
Ya ce:
“Akwai jita-jitar cewa na koma APC. Ba zan je ko’ina ba, amma muna da matsaloli a PDP. Siyasa abu ne mai iya sauyawa.
"Za mu iya kasancewa a ko’ina, amma ba za mu yi wauta ba. Za mu dauki dukkan matakai cikin dabara.”

Source: Twitter
Alkawarin Gwamna Bala ga ma'aikata a Bauchi
Gwamnan har ila yau, ya sha alwashin biyan albashi a kan lokaci da kuma tabbatar da biyan giratuti kafin kammala wa'adin mulkinsa a jihar Bauchi.
Bala Mohammed ya shawarci ma'akatan gwamnati da su yi aiki tukuru domin tallafawa gwamnati saboda samar da ababan more rayuwa.
"Ina kira ga ma'aikatan gwamnati da sauran masu rike da mukaman gwamnati da mu yi amfani da abin da muke da shi a kasa yadda ya dace.
"Za mu ci gaba da samar da ababan more rayuwa ga al'umma domin samar da rayuwa mai inganci.
"Na yi alkawarin kafin na bar mulki zan yi kokari na biya dukan basukan da na gada na giratuti ga tsofaffin ma'aikata."
- Gwamna Bala Mohammed
An yi ta yada Gwamna Bala zai koma APC
A baya, mun sanar da ku cewa wasu majiyoyi sun ce Gwamna Bala Mohammed ya kammala shirin barin PDP zuwa APC a bayan tattaunawa da Shugaba Bola Tinubu kan makomarsa.
An ruwaito cewa Shugaba Tinubu ya gargaɗi Bala Mohammed cewa ba zai ba shi ikon zaɓar wanda zai gaje shi ba koda ya koma jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya.
An kuma umarci Gwamna Bala ya ba ɗan shugaba ƙasa Seyi Tinubu haƙuri kafin a amince da buƙatarsa ta shiga cikin jam'iyyar mai mulki a ƙasa.
Asali: Legit.ng

