PDP ko APC?: INEC Ta Fadi Jam'iyyar da Ta Lashe Zaben Ciyaman a Bwari, Abuja
- Joshua Ishaku na jam'iyyar APC ya lashe zaben kujerar shugaban karamar hukumar Bwari da kuri'u 18,466 a zaben ranar Asabar
- Hukumar INEC ta bayyana cewa jam'iyyar ADC ce ta zo na biyu a zaben yayin da jam'iyyar ZLP ta zo matsayi na uku a zaben
- An gudanar da zaben ne a mazabu 10 dake karkashin Bwari wadanda suka hada da Kubwa da Dutse da Ushafa da Bwari ta Tsakiya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta ayyana Joshua Ishaku na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙaramar hukumar Bwari.
Babban jami'in tattara sakamakon zaɓen, Farfesa Mohammed Nurudeen, ya bayyana sakamakon ne a ranar Lahadi, inda ya tabbatar da cewa Ishaku ya samu jimillar ƙuri'u 18,466.

Source: Getty Images
APC ta lashe zaben ciyaman a Bwari
Farfesan ya bayyana cewa Joshua Ishaku ya cika dukkan sharuɗɗan da doka ta tanada, don haka aka ayyana shi a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙaramar hukumar Bwari, in ji rahoton Premium Times.
Bayan jam'iyyar APC da ta zo ɗaya a zaben, ɗan takarar jam'iyyar ADC ne ya zo na biyu da ƙuri'u 4,254, yayin da jam'iyyar Zenith Labour (ZLP) ta zo ta uku da ƙuri'u 3,515.
Wannan nasara ta APC na zuwa ne bayan wani gagarumin sauyin siyasa da aka samu a yankin kafin ranar zaɓen ta ranar Asabar.
Nasarar APC a mazabu 10 na Bwari
Farfesa Mohammed Nurudeen ya ce:
"Joshua Ishaku, bayan ya cika sharuɗɗan doka, an ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara kuma zaɓaɓɓen shugaban karamar hukumar Bwari."
Kamfanin dillancin labarai na ƙasa (NAN) ya ruwaito cewa an gudanar da zaɓen ne a dukkan mazabu goma da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar Bwari.
Mazabun sun haɗa da Igu, Shere, Dutse, Ushafa, Byazhin, Kuduru, Kubwa, Usuma, Bwari Central da kuma Kawu a yau.

Source: Twitter
Tasirin janyewar 'dan takarar PDP
Idan za a iya tunawa, Legit Hausa ta rahoto cewa ɗan takarar jam'iyyar PDP na yankin, Julius Adamu, ya janye daga takara saura kwanaki biyu zaɓen domin marawa ɗan takarar APC baya.
Wannan mataki, wanda ministan birnin tarayya Nyesom Wike ya shiga tsakani, ya taka rawar gani sosai wajen baiwa jam'iyyar APC damar samun wannan gagarumar nasara yau.
Mazauna yankin Bwari da Kubwa yanzu haka suna cikin yanayi na murna da kuma tsammanin ganin irin ci gaban da sabuwar gwamnatin za ta kawo.
Joshua Ishaku ya yi alƙawarin inganta hanyoyin mota da samar da ababen more rayuwa ga mazauna yankin a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe yanzu.
PDP ta lashe zaben ciyaman a Abuja
A wani labarin, mun ruwaito cewa, Mohammed Kasim na jam'iyyar PDP ya lashe zaben ciyaman na karamar hukumar Gwagwalada da kuri'u 22,165.

Kara karanta wannan
NNPP da manyan jam'iyyu 2 da ba a ga tambarinsu a takardar zaben cike gurbin Kano ba
Kasim ya samu ƙuri'u 22,165, inda ya doke babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar APC, Yahaya Shehu, wanda ya samu ƙuri'u 17,788.
Babban jami'in tattara sakamakon zaɓen, Philip Akpen, ya bayyana cewa an gudanar da zaɓen cikin lumana a dukkanin yankunan ƙaramar hukumar.
Asali: Legit.ng

