Ana cikin Azumi, Sanata Rufai Hanga Ya Burma Matsala a Kotun Musulunci a Kano

Ana cikin Azumi, Sanata Rufai Hanga Ya Burma Matsala a Kotun Musulunci a Kano

  • An maka Sanata Rufa'i Hanga a gaban kotun shari'ar Musulunci da ke Shahuci a cikin birnin Kano kan zargin kin biyan hakkokin yakin neman zaben 2023
  • Masu kara sun gabatar da hujjoji a gaban kotu, inda suka nemi Sanata Hanga, mai wakiltar Kano ta Tsakiya a majalisar dattawa ya biya su N124,800,070
  • Da aka zauna a kotu, lauyan Sanata Hanga ya roki kotu da ta yi watsi da karar gaba daya amma Mai Shari'a Muhammad Sani ya ki amincewa da hakan

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Babbar Kotun Shari’a da ke Shahuci a Kano, ta fara sauraron ƙarar da aka shigar kan Sanata Rufai Sani Hanga, mai wakiltar Kano ta Tsakiya a Majalisar Dattawa.

Shari’ar ta shafi zargin Sanata Rufai Hanga da rashin biyan kuɗin ayyukan kamfen da suka kai kusan N124,800,070.

Kara karanta wannan

"Ana buƙatar taimako": Shehu Sani ya yi maraba da girke sojojin Amurka a Najeriya

Sanata Rufa'i Hanga
Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya, Rufai Sani Hanga Hoto: Rufai Sani Hanga
Source: Twitter

Jaridar Tribune Nigeria ta ruwaito cewa an shigar da wannan kara ne gaban Mai Shari'a Muhammad Sani na kotun shari'ar musulunci.

Abin da masu ƙarar Rufai Hanga ke zargi

Isa Ado Medoya da wasu mutane sun shigar da ƙara bisa zargin cewa sun yi wa Rufa'i Hangankamfen kamar yadda doka ta amince a lokacin zaɓen sanatan, amma har yanzu ba a biya su haƙƙinsu ba.

Alƙali Muhammad Sani ya buɗe zaman kotun inda lauyan masu ƙara ya gabatar da hujjojin da gabatar da karar. A cewar masu ƙara, kuɗin da suke nema diyya ne kan ayyukan da suka yi a lokacin kamfen.

An fara gabatar da hujjoji kan Sanata Hanga

Lauyan masu ƙara, Barrista Abbas Sani Abubakar Mandawari, ya gabatar da wasu takardu da hujjoji da nufin nuna yadda aka gudanar da aikin.

Sai dai ya sanar da kotu cewa yana buƙatar ƙarin lokaci domin tuntuɓar wadanda yake karewa da tsara wasu takardu da suka rage, tare da neman a ba su lokaci domin tabbatar da wasu bayanai.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: Jami'an DSS sun cafke El Rufai a harabar ofishin EFCC

Martanin ɓangaren Sanata Rufa'i Hanga

Lauyan wanda ake ƙara ya yi fatali buƙatar, yana mai cewa alamar rashin shiri ce daga ɓangaren masu ƙara.

Ya roƙi kotu ta yi watsi da ƙarar, yana mai cewa jinkirin ya nuna ba su shirya bin shari’ar yadda ya kamata ba, in ji rahoton Daily Post.

Sai dai kotun ta ƙi amincewa da roƙon yin watsi da ƙarar, inda ta yanke hukuncin bai wa masu ƙara ƙarin lokaci domin su karisa gabatar da takardunsu.

Rufai Hanga.
Sanatan Kano ta Tsakiya, Rufa'i Sani Hanga a ofishinsa da ke zauren Majalisar dattawa Hoto: Rufai Sani Hanga
Source: Facebook

Kotun musulunci ta ɗage zaman shari’ar

Alƙalin ya jaddada muhimmancin bai wa kowane ɓangare cikakkiyar dama domin gabatar da hujjoji da bayanansa yadda ya kamata.

An ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 21 ga Afrilu, 2026, inda ake sa ran masu ƙara za su gabatar da cikakkun takardu, sannan lauyan wanda ake ƙara zai miƙa martaninsa a hukumance.

Sanata Kawu ya dura kan Ado Doguwa

A wani rahoton, kun ji cewa Sanata Kawu Sumaila ya roki jama’a su guji mayar wa Alhassan Ado Doguwa martani, yana cewa yana fuskantar wata matsala.

Kara karanta wannan

Abin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fada da ya koma APC

Kawu Sumaila ya yi martanin ne bayan mutane suna ta kiransa kan lamarin Hon. Doguwa saboda maganganu da ya yi a wani taron APC a Kano.

'Dan majalisar kudancin Kano ya ce Alhassan Doguwa ba zai fahimci yana cikin wani hali ba saboda haka lalurar take, inda ya ce addu'a da hakuri yake bukata.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262