Atiku Ya Ziyarci El Rufai da Dare bayan Ya Sha da Kyar a Filin Jirgin Sama
- Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya kai ziyara ta musamman ga Nasir El-Rufai bayan hargitsin a filin jirgin sama
- Atiku ya nuna masa cikakken goyon baya, yana zargin gwamnatin Bola Tinubu da kokarin kawo mulkin kama-karya
- Ziyarar na zuwa ne bayan kokarin jami’an tsaro na cafke El-Rufai, lamarin da ya haddasa ce-ce-ku-ce da rikici
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Kaduna - Jim kadan bayan hargitsin da ya faru a filin jirgin sama, Atiku Abubakar ya kai ziyara ta musamman ga Nasir El-Rufai a gidansa.
Atiku ya kai ziyara ga El-Rufai ne domin nuna masa goyon baya dari bisa dari bayan abin da ya faru da shi a filin jirgin sama.

Source: Facebook
Hakan na cikin wani bidiyo da Abdulaziz Na'ibi Abubakar, daya daga cikin masoyan Atiku ya wallafa a shafin X a daren jiya Alamis 12 ga watan Faburairun 2026.
An yi yunkurin cafke El-Rufai
Wannan ziyara na zuwa ne bayan kokarin da jam'ian tsaro suka yi na cafke tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai a Abuja.
Lamarin ya hargitse yayin da El-Rufai da magoya bayansa suka ki amincewa da shirin cafke shi jim kadan bayan shigowa Najeriya daga ketare.
Hakan bai rasa nasaba da yawan sukar gwamnatin Bola Tinubu da tsohon gwamnan ke yi wanda a yan kwanakin nan abin sai karuwa yake yi.
Daga cikin hirarrakin da yake yi, ya ambaci cewa ana shirin kama shi idan ya dawo Najeriya wanda kuma hakan ya tabbata.
Atiku ya ziyarci El-Rufai a gidansa
Yayin ziyarar, Atiku Abubakar ya bayyana goyon bayansa ga El-Rufai dari bisa dari game da halin da ake ciki da kuma lalacewar kasa.
Ya ce:
"Wannan gwamnati ba ta da niyyar ta bar dimukradiyya ta dore, tana son kawo mana mulkin kama-karya da na cin mutunci yadda ba wani dan Adam da yake da wani 'yanci.
"Mu 'yantattu ne, haka Allah ya halicce um, ba mu ga dalilin da za ta dauke mana hakkin da Allah ya ba mu ba.
"Malam ina mai tabbatar maka kana da cikakken goyon bayanmu, dukanmu mun amince a bin tafarkin dimukradiyya da dokokin kasa."

Source: Twitter
Tabbacin da Atiku ya ba El-Rufai
Atiku ya ba El-Rufai tabbacin cewa za su ci gaba da ba shi goyon baya da kuma tsare mutuncinsa da na magoya bayansu.
"Mu na shirye mu ba ka kowane irin taimako, mu tsare mutuncinka da mutuncin magoya bayanmu, muna yi maka barka da dawowa.
"Za mu ci gaba da wannan yaki na tabbatar da yanci da dorewar dimukradiyya, wannan APC mu muka kafa ta, amma sun kauce hanya shi yasa muka fita."
- Atiku Abubakar
El-Rufai zai ziyarci ofishin EFCC a Abuja
Mun ba ku labarin cewa Lauyan Malam Nasiru El-Rufai ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan zai amsa gayyatar EFCC a ranar Litinin, 18 ga watan Fabrairu, 2026.
Barista Ubong Esop Akpan ya bayyana hakan ne jim kadan bayan yunkurin da jami'an tsaro suka yi na kama El-Rufai a filin jirgin sama a Abuja.
Ya ce abin da jami'an tsaron suka yi ya saba wa kundin tsarin mulki, yana mai cewa sun sanar da EFCC halin da ake ciki tun farko.
Asali: Legit.ng

