Magoya Bayan Kwankwaso Sun Gano Abokin Takarar da Ya Dace da Shi a Zaben 2027

Magoya Bayan Kwankwaso Sun Gano Abokin Takarar da Ya Dace da Shi a Zaben 2027

  • Kungiyoyin magoya bayan jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, sun fara maida hankali kan zaben 2027
  • Sun bayyana hadakar da ya kamata Kwankwaso ya shiga domin samar da tikiti mai kafi wanda zai iya kifar da Mai girma Bola Tinubu
  • Hakazalika, sun kuma karyata batun cewa madugun na Kwankwasiyya ya gabatar da wasu sharuda domin shiga jam'iyyar APC

​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Kano - Magoya bayan jagoran jam'iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, sun ba da shawara kan zaben 2027.

Magoya bayan na Kwankwaso sun ba da shawarar a samar da haɗaɗɗen tikitin takarar shugaban ƙasa na Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso gabanin zaɓen shekarar 2027.

Magoya bayan Kwankwaso sun ba shi shawara kan zaben 2027
Tsohon dan takarar shugaban kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso
Source: Facebook

Tashar Arise News ta ce Abba Sadauki Gwale ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a madadin ƙungiyoyin goyon baya a Kano ranar Juma’a, 6 ga watan Fabrairun 2026.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya firgita mutanen Abba Kabir bayan tara dandazon jama'a a Kano

Ana so Kwankwaso ya hade da Peter Obi

Abba Sadauki Gwale ya ce wannan shawara tana nuna burin magoya bayan Kwankwaso na mara baya ga wata haɗin gwiwa da za ta iya ceto Najeriya daga matsalolin da take ciki a halin yanzu.

Yaa ce tikitin Obi–Kwankwaso na iya fitowa ƙarƙashin kowace jam’iyya ta siyasa, yana mai jaddada cewa yanayin siyasar da ake ciki yanzu na nuna sauyin ra’ayin jama’a a fili, jaridar Thisday ta kawo labarin.

"Idan aka ba wannan haɗin gwiwa dama a zaɓen da ke tafe, Najeriya za ta samu ci gaba. Mun gaji da rashin tsaro, yunwa da talauci.”

- Abba Sadauki Gwale

Amfanin tikitin Obi da Kwankwaso

A cewarsa, manufar wannan haɗin gwiwa ita ce haɗa ƙarfi da goyon bayan Obi a Kudancin Najeriya da kuma gagarumin farin jinin Kwankwaso a Arewa, domin samar da babbar haɗakar da za ta iya kalubalantar jam’iyyar da ke mulki.

Abba Sadauki Gwale ya ce wannan haɗin gwiwa tana da niyyar ƙwace mulki daga Jam’iyyar APC da jagoranta Bola Ahmed Tinubu, tare da kawo sauyi na gaske ga rayuwar ’yan Najeriya.

Kara karanta wannan

Bayan raba gari a siyasa, Abba da Kwankwaso sun gwada farin jininsu a Kano

Ya ƙara da cewa duka Peter Obi da Kwankwaso sun dade suna jaddada manufofi da suka shafi inganta jin daɗin talakawa, yana mai cewa saƙonsu na kawo gyara yana karɓuwa sosai a tsakanin al’umma.

“Yayin da shekarar 2027 ke ƙaratowa, idanu suna kan haɗin gwiwar Obi–Kwankwaso domin a ga yadda za ta sauya wannan ƙwarin gwiwa zuwa ƙuri’u."

- Abba Sadauki Gwale

An bukaci Kwankwaso ya hade da Peter Obi
Tsohon dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, Peter Obi Hoto: @PeterObi
Source: Facebook

Batun komawar Kwankwaso APC

Da yake mayar da martani kan jita-jitar da ke cewa Kwankwaso ya gabatar da wasu sharuɗa domin shiga APC, Gwale ya ƙaryata hakan gaba ɗaya, yana mai cewa wannan magana ba ta da tushe.

Ya jaddada cewa duk wata shawarar siyasar Kwankwaso tana tafiya ne bisa muradin magoya bayansa a faɗin ƙasar nan, kuma har yanzu Kwankwaso na da babban goyon bayan jama’a, musamman a Kano da sauran jihohi, duk da sauye-sauyen siyasa da ake gani a baya-bayan nan.

Kwankwaso ya gigita mutanen Abba

A wani labarin kuma, kun ji cewa dandazon mutanen da Rabiu Musa Kwankwaso, ya tara a wajen wasu tarurruka, ta sanya mutanen Gwamna Abba Kabir Yusuf cikin firgici.

Kara karanta wannan

An tafi da Kwankwaso zuwa kasar waje bayan fama da rashin lafiya? An ji gaskiyar zance

Wasu daga cikinsu sun roki Gwamna Abba Kabir Yusuf da ya jawo Kwankwaso cikin tafiyar gwamnati, ko kuma a samu sulhu tsakaninsu.

Haka kuma wasu na ganin cewa idan ba a yi taka tsan-tsan ba, za a iya samun gwamna mai jiniya da gwamna mai jama'a a Kano.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng