A Karshe, An Ji Matsayar Murtala Sule Garo kan Sauya Shekar Gwamna Abba zuwa APC

A Karshe, An Ji Matsayar Murtala Sule Garo kan Sauya Shekar Gwamna Abba zuwa APC

  • Murtala Sule Garo ya yi maraba da sauya shekar Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf daga jam'iyyar NNPP zuwa APC mai mulkin kasa
  • Garo, wanda ya yi takarar mataimakin gwamna a zaben 2023 karkashin inuwar APC, ya ce Abba ya dauki matakin da ya dace a siyasance
  • Tsohon kwamishinan ya ce matakin da gwamna ya dauka ya nuna irin gogewarsa a fagen siyasa, wansa hakan zai amfanar da jihar Kano

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - 'Dan takarar mataimakin gwamna na APC a zaben 2023, Murtala Sule Garo, ya yi maraba da Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, zuwa jam’iyyar.

Murtala Garo ya bayyana sauya shekar Gwamma Abba daga NNPP zuwa APC a matsayin mataki na samar da daidaiton siyasa da dorewar ci gaba a jihar Kano.

Kara karanta wannan

Ana batun sauya shekar Abba, za a bayyana asalin wadanda suka ci amanar Kano

Murtala Sule Garo.
Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan Kano, Mutala Sule Garo Hoto: Mutala Sule Garo
Source: Facebook

Garo, wanda tsohon Kwamishinan Kananan Hukumomi da Masarautu ne, ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa ranar Talata, kamar yadda Punch ta rahoto.

Murtala Sule Garo ya yi maraba da Abba

Hon. Murtala Garo ya ce matakin gwamnan na komawa jam’iyya mai mulki ya nuna kwarewarsa a fagen siyasa da kuma hangen nesa, a daidai lokacin da Kano da ma kasa baki daya ke bukatar hadin kai da shugabanci na gari.

“Ina lale maraba da Mai girma gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, zuwa cikin jam’iyyar APC."
"Wannan wani babban mataki ne abin a yaba a kokarinmu na neman daidaiton siyasa, shugabanci na bai-daya, da dorewar ci gaba a jihar Kano,” in ji sanarwar.

Garo ya jinjina wa Gwamna Abba Kabir

Murtala Sule Garo ya yaba da salon shugabancin Abba Gida-Gida, inda ya lura cewa natsuwarsa da jajircewarsa aun nuna cewa a shirye yake ya sanya muradun zaman lafiya da ci gaba gaba da na jam'iyya.

Kara karanta wannan

Kano: Abba ya yi sababbin nade nade bayan ya koma APC

"Ta hanyar wannan mataki da ya dauka, mai girma gwamna ya nuna karfin ikon ketare rabuwar kawuna na jam’iyya domin tabbatar da zaman lafiya, ci gaba, da hadin kai,” in ji Garo.

Jigon a APC ya kara da cewa hadewar da gwamnan ya yi da jam’iyya mai mulki ya nuna karara cewa ya fahimci yanayin siyasa da tattalin arziki da jihar Kano da ma kasar baki daya ke fuskanta.

Murtala Garo zai hada kai da Abba

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa shigowar Abba cikin APC zai kara karfafa shirye-shiryen gyara jam’iyyar, sannan zai inganta hadin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar Kano da ta tarayya, cewar rahoton Daily Post

Gwamna Abba.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf a fadar gwamnati Hoto: Sanusi Bature
Source: Facebook

Garo ya sake jaddada biyayyarsa ga APC, inda ya yi alkawarin yin aiki tare da gwamnan da sauran masu ruwa da tsaki domin ciyar da Kano gaba, hadin kan siyasa, da manufofin da suka dace da jama'a a fadin jihar.

Wannan mataki na Murtala Garo ya janyo hankalin mutane da yawa, ganin yadda zaben 2023 ya kasance cike da hamayya tsakaninsa da Gwamna Abba.

Kwankwaso ya soki tafiyar Gwamna Abba

A wani rahoton, kun ji cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya nuna takaicinsa kan yadda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bar jam'iyyar NNPP.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya tuna bibiyar alkalan kotun koli da ya yi saboda Abba a zaben 2019

Sanata Kwankwaso ya ce sau da dama yana yin tunani a kan abin da ya faru tsakaninsa da Gwamna Abba Kabir Yusuf, yana tambayar kansa ko shi ne ya yi laifi ko jam’iyya.

Ya ce duk da wannan nazari da yake yi, har yanzu bai samu amsar da za ta gamsar da shi ba, lamarin da ke ƙara nuna masa cewa sauya sheƙar gwamnan ta zo ne ba tare da dalili mai karfi ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262