An Zo Wajen: Gwamna Zulum Ya Tsage Gaskiya kan Wanda Zai Gaje Shi a 2027

An Zo Wajen: Gwamna Zulum Ya Tsage Gaskiya kan Wanda Zai Gaje Shi a 2027

  • Masu ruwa da tsaki na jam'iyyar APC a Borno, sun gudanar da muhimmin taro a birnin Maiduguri, babban birnin jihar
  • Gwamnan jihar Borno ya yi tsokaci a wurin taron kan wanda zai gaje shi bayan ya kammalaa wa'adinsa a shekarar 2027
  • Hakazalika, Gwamna Zulum ya kuma kafa kwamitin da zai jagoranci aikin sasanta 'ya'yan jam'iyyyar APC a jihar Borno

​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Borno - Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya yi magana kan wanda zai gaje shi a zaben shekarar 2027.

Gwamna Babagana Zulum ya bayyana cewa bai san wanda zai gaje shi ba bayan karewar wa’adinsa a watan Mayun 2027.

Gwamna Zulum ya ce bai da wanda zai gaje shi
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum Hoto: Dauda Iliya
Source: Facebook

Jaridar Vanguard ta ce Gwamna Zulum ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, 25 ga watan Janairun 2026 yayin wani muhimmin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC.

Kara karanta wannan

Abin da Kwankwaso da mutanen Kano suka dauki hadewar Gwamna Abba da Ganduje a APC

Masu ruwa da tsaki na APC sun yi taro

An gudanar da muhimmin taron ne a babban dakin taro na fadar gwamnatin jihar Borno da ke birnin Maiduguri, jaridar Leadership ta kawo labarin.

Gwamnan ya jaddada cewa gwamnatinsa ta maida hankali ne wajen ƙarfafa tsaro da kuma samar da ci gaban da al’ummar jihar ke buƙata.

Da yake jawabi ga shugabannin jam’iyya, zaɓaɓɓun jami’ai da mambobi, Zulum ya sake nanata matsayinsa na tabbatar da adalci, gaskiya da daidaito a tsarin zaɓen shugabannin jam’iyya a yayin zabubbukan da ke tafe.

Gwamna Zulum ya kuma yi watsi da rade-radin da ke cewa yana da tasiri wajen tsara tikitin jam’iyyar a nan gaba.

Wane ne zai gaji Gwamna Babagana Zulum?

Ya bayyana a fili cewa bai tsayar da wani ɗan takara ba, ko don muƙaman jam’iyya ko kuma kowane mukamin zaɓe ba.

“Ba ni da ɗan takara a kowanne matsayi, kuma ban san wanda zai gaje ni ba. Na damƙa zaɓin shugabanni ga Allah Maɗaukakin Sarki, bisa ga tsarin dimokiraɗiyya da muradin mambobin jam’iyya da al’ummar jihar Borno."

Kara karanta wannan

Tsofaffin 'yan majalisa sun yi watsi da mara wa Tinubu baya a zaben 2027

- Gwamna Babagana Umara Zulum

Zulum ya kafa kwamitoci kan ayyukan APC

Gwamnan ya kuma kafa kwamitoci biyu domin kara inganta rajistar APC ta yanar gizo da kuma sasanta mambobin jam’iyyar.

Kwamitin mai mutum 10 zai kasance karkashin jagorancin tsohon jakadan Najeriya a kasar China, Baba Ahmed Jidda, kuma ya kunshi mambobi daga mazabun sanatoci uku na jihar.

Ambasada Baba Ahmed Jidda mai shekaru fiye da 70 a duniya ya rike mukamai da dama a karamar hukumarsa ta Marte, jihar Borno da kuma gwamnatin tarayya.

Jiga-jigan APC sun halarci taro

Taron ya samu halartar Mukaddashin gwamnan jihar, Umar Usman Kadafur; tsohon Gwamnan jihar Borno, Maina Ma’aji Lawan; Mataimakin shugaban APC na kasa, Ali Bukar Dalori; Shugaban APC na Jihar Borno, Bello Ayuba.

Gwamna Zulum ya kafa kwamitoci kan ayyukan APC
Gwamna Babagana Umara Zulum tare da wasu jiga-jigan APC a wurin taron jam'iyyar a Borno Hoto: Dauda Iliya
Source: Facebook

Sauran mahalarta taron sun hada da tsofaffin Mataimakan gwamnan jihar uku da suka haɗa da Ali Abubakar Jatau, Adamu Shettim Dibal da Usman Mamman Durkwa.

Hakazalika, babban mai tsawatarwa na Majalisar dattawa, Mohammed Tahir Monguno; Sanata Kaka Shehu Lawan; da ’yan majalisar wakilai 10, ciki har da Midala Balami wanda ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, sun halarci taron.

Kara karanta wannan

"Za su sha mamaki"; Gwamna Makinde ya hango makomar PDP a zaben 2027

Gwamna Abba ya koma jam'iyyar APC

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sauya sheka zuwa jam'iyyar APC a hukumance bayan ficewa daga NNPP.

Gwamna Abba ya shiga APC ne a gaban tsohon shugaban jam’iyyar na kasa kuma tsohon gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Hakazalika, Gwamna Abba ya jaddada cewa dalilin komawarsa APC shi ne domin samar da kyakkyawar dangantaka da hadin kai tsakanin Kano da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng