Ta Faru Ta Kare: Gwamna Abba Ya Shiga Jam'iyyar APC a gaban Ganduje da Barau

Ta Faru Ta Kare: Gwamna Abba Ya Shiga Jam'iyyar APC a gaban Ganduje da Barau

  • Bayan tsawon lokaci ana tirka-tirka a siyasar jihar Kano, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya koma jam''iyyar APC mai mulkin Najeriya a hukumance
  • Tsohon shugaban APC na kasa, Abdullahi Ganduje da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin ne suka karbi Gwamna Abba yau Litinin
  • Wannan na zuwa ne kwanaki uku bayan Abba ya mika takardar ficewa daga jam'iyyar NNPP a mazabarsa da ke karamar hukumar Gwale a Kano

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya koma jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya a hukumance a yau, Litinin, 26 ga watan Janairun 2026.

Gwamna Abba, wanda ake wa lakabi da Abba Gida-gida, ya sanar da hakan ne a wani gagarumin taro da aka shirya a babban dakin taron da ke gidan gwamnatin jihar Kano.

Kara karanta wannan

Babbar magana: Gwamna Abba na shiga APC, Ganduje ya fadi jagoran jam'iyyar a Kano

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.
Gwamna Abba Kabir Yusuf lokacin da Sanata Barau Jibrin da Ganduje suka karbe shi zuwa APC Hoto: Sanusi Bature
Source: Facebook

Gwamna Abba ya koma APC a hukumance

Rahoton TVC News ya nuna cewa Gwamna Abba ya shiga APC ne a gaban tsohon shugaban jam’iyyar na kasa kuma tsohon gwamnan Kano, Dr. bdullahi Umar Ganduje.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Kawu Sumaila da Karamin Ministan Gidaje da Raya Birane, Yusuf Abdullahi Ata da wasu manyan baki sun halarci taron.

Abba ya jaddada cewa dalilin komawarsa APC shi ne domin samar da kyakkyawar dangantaka da hadin kai tsakanin Kano da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Jawabin Gwamna Abba a taron shiga APC

Gwamnan ya bayyana cewa burinsa na samar da hadin kai, kwanciyar hankali, da kuma hanzarta kawo ci gaba a fadin jihar ne ya ja shi zuwa APC.

"Idan Allah ya yarda (bayan komawarmu APC) zq ku ga canji, za ku ga karin ayyuka, za ku ga ci gaba, ba za mu zauna a cikin duhu mu zama makafi fa, lokaci ya yi da za su hada kai da gwamnatin tarayya.

Kara karanta wannan

Jita jita ta kare, 'yan majalisa 22 sun sauya sheka daga NNPP zuwa APC a Kano

"Za ku ga hadin kan da baku taba gani ba a Kano, za ku ga ayyukan ci gaba sosai," in ji Gwamna Abba.
Gwamna Abba Kabir Yusuf na Kano.
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf na jagorantar taron SEC Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Idan za a tuna, Abba ya fice daga jam’iyyar NNPP a ranar Juma’a, inda ya dora laifin ficewarsa kan tsananin rikicin cikin gida da kuma takaddamar shugabanci da ta dade tana addabar jam’iyyar.

A cewarsa, babban abin da ya sa a gaba shi ne samar da shugabanci na gari da kuma mika romon dimokuradiyya ga mazauna jihar Kano, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

Masu sharhi kan al’amuran siyasa na ganin wannanataki na Abba na iya sauya fasalin siyasar Kano da ma Arewa gaba ɗaya, yayin da ake sa ran APC za ta ƙara ƙarfi a jihar.

An kafa tutocin APC a gidan gwamnatin Kano

A wani labarin, kun ji cewa rahotanni sun nuna cewa an kawata fadar gwamnatin jihar Kano da sababbin tutocin jam'iyyar APC bayan cire na NNPP.

Bayanai sun nuna cewa tun daga kofar shiga gidan gwamnatin har zuwa cikin ofisoshi, duk an maye gurbin tutocin NNPP da na APC.

Gwamnatin Kano dai ta bayyana sauya shekar Gwamna Abba zuwa APC a matsayin komawa gida kasancewar ya taba zama a jam'iyyar a shekarar 2014.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262