Abin da Aka Yi Wa Tutar NNPP a Gidan Gwamnatin Kano Ya Ja Hankalin Mutane, Bidiyo Ya Fito
- An cire tutar NNPP daga fadar gwamnatin jihar Kano bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar
- Wannan ci gaba na zuwa ne kwanaki kadan bayan gwamnan ya gana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadarsa da ke Abuja
- Bidiyon cire tutar ya ja hankalin mutane da dama a kafafen sada zumunta, inda wasu suka bayyana lamarin da halin 'yan siyasa
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - A yau Juma'a, 23 ga watan Janairu, 2025, Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ta sanar da ficewarsa daga jam'iyyar NNPP a hukumance
Gwamna Abba ya tabbatar da haka ne a wata wasika da ya aike wa shugaban NNPP na mazabar Diso-Chiranchi da ke karamar hukumar Gwale a jihar Kano.

Source: Facebook
Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Faceook yau Juma'a.
An cire tutar NNPP a gidan gwamnatin Kano
Sai dai jim kadan bayan wannan sanarwa, wani faifan bidiyo ya fara yawo a kafafen sada zumunta, inda aka ga wani jami'i ya fitar da tutar NNPP daga fadar gwamnatin Kano
Faifan bidiyon ya nuna yadda mutumin ya nannade tutar NNPP, sannan ya dauke ta ya yi waje da ita a gidan gwamnatin da ke cikin birnin Kano, lamarin da ya kara tabbatar da ficewar Abba Gida-Gida.
Har yanzu dai ba a ji ta bakin jagoran jam'iyyar NNPP na kasa, Injiniya Rabiu iMusa Kwankwaso kan wannan mataki da Abba ya dauka ba.
Sai dai ana tsammanin Gwamna Abba zai sanar da komawa jam'iyyar APC a hukumance nan ba da jimawa ba.
Wani mai amfani da shafin X, Imran Muhammad ya wallafa faifan bidiyon lokacin da aka cire tutar NNPP daga gidan gwamnatin Kano.
Martanin mutane kan cire tutar NNPP
Bayan wannan bidiyo ya fara yawo, 'yan Najeriya sun tofa albarkacin bakinsu kan cire tutar NNPP da kuma ficewar Gwamna Abba daga jam'iyyar. Mun tattaro muku wasu daga ciki:
Hephziba Behulah ya ce:
"Za ka yi nadama, su 'yan siyasa ba su da kunya, 'yan Najeriya kuma ba su da kwalwalwar rike abu, amma duk da haka ku rubuta wannan ku ajiye."
Maryam Cissey ta ce:
"Lokacin da na gaya muku gwamnan jihar Kano bai san abin da yake yi ba, zagi na kuka yi. Ku gan shi yanzu bayan ya kasa kawo wani babba abin ci gaba a jihar Kano.
Hamman Atiku ya ce:
"Ku lura da kyau, shi kan sa wanda ya cire tutar NNPP, ba jar hula ba ce a kansa."

Source: Facebook
Gwamna Abba zai tura tawaga ga Kwankwaso
A wani rahoton, kun ji cewa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, zai kafa kwamitin jakadu don sanar da ubangidansa, Rabiu Kwankwaso sauyin sheƙarsa zuwa APC.
Wata majiya mai tushe da ta halarci wata ganawar sirri da aka gudanar da daddare ta shaida wa manema labarai matsayar da aka cimma game da batun sauya sheka.
Majiyar ta ce Gwamnan ya amince cewa, bisa ladabi da girmamawa, ya dace a sanar da Kwankwaso a hukumance kafin a bayyana sauyin sheƙar.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

