Lissafi Zai Iya Canzawa, Tinubu Ya Shiga Ganawa da Gwamnan PDP a Fadar Shugaban Kasa
- Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ganawa da gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde a fadar shugaban kasa da ke birnin tarayya Abuja
- Wannan ganawa na zuwa ne makonni kadan bayan gwamnan Filato, Barista Caleb Mutfwang ya sauya sheka daga PDP zuwa APC
- Gwamna Makinde na daya daga cikin tawagar G-5, wacce ta yi wa Bola Tinubu aiki a zaben shugaban kasa na shekarar 2023
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya kai ziyara fadar shugaban kasa da birnin tarayya Abuja yau Alhamis, 22 ga watan Janairu, 2025.
Rahotanni sun nuna cewa daga zuwan Gwamna Makinde, ya wuce kai tsaye ya shiga ganawa da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a cikin Aso Rock.

Source: Twitter
Jaridar The Nation ta rahoto cewa wannan ganawa ta sake haifar da sabon hasashe na siyasa a daidai lokacin da ake ci gaba da sauya sheƙa kafin zaɓen 2027.
Bola Tinubu ya zauna da Gwamnan Oyo
Ganawar Tinubu da Gwamna Makinde, wanda yana daya daga cikin manyan jagororin jam’iyyar adawa ta PDP, na zuwa ne kwanaki kadan bayan Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang ya koma APC.
Gwamnan Oyo na daga cikin gwamnonin PDP guda biyar da aka fi sani da G-5, waɗanda suka yi adawa da Atiku Abubakar a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP a zaɓen 2023.
Sauran mambobin G-5 sun haɗa da tsohon Gwamnan Jihar Rivers kuma Ministan Abuja na yanzu, Nyesom Wike; tsohon Gwamnan Benue, Samuel Ortom; tsohon Gwamnan Enugu, Ifeanyi Ugwuanyi; da tsohon Gwamnan Abia, Okezie Ikpeazu.
Makinde da Wike sun samu sabani
Sai dai daga baya, Gwamna Makinde da Wike sun samu saɓani a tsakaninsu, lamarin da ya jawo suka rika musayar yawu musamman kan rigingimun da suka addabi PDP, cewar Vanguard.
A wata hira da ya yi kwanan nan, Makinde ya ce rikicin ya samo asali ne daga wata ganawa da suka yi da Tinubu, inda Wike ya yi alƙawarin dukusar da PDP domin shugaban kasa ya yi tazarce a 2027.
“Mun yi wani taro da Shugaban Ƙasa tare da Wike da wasu mutane, sai Wike ya ce wa Shugaban Ƙasa zai rike masa PDP don ya samu sauki a 2027. Sai muka tashi, na tambaye shi, shin mun amince da wannan?” in ji Makinde.

Source: Twitter
Makinde ya jaddada cewa duk da Wike na da ‘yancin goyon bayan sake zaɓen Shugaba Tinubu, sauran ‘yan PDP ma suna da ‘yancin ƙin amincewa da duk wani yunkuri da zai raunana dimokuraɗiyya mai jam’iyyu da yawa.
Mukami sai 'dan jam'iyyarmu - Shugaban APC
A karshen makon nan ne rahoto ya gabata cewa APC ta ce ta shirya dabarun da za su ba ta nasara a babban zaben 2027 wanda ake sa Bola Tinubu zai shiga.
Farfesa Yilwatda Nentawe a matsayin Shugaban APC ya jero dabarun cin zabe, ciki har da jawo matasan Najeriya a jiki domin ganin yadda za su sake mara masu baya.
Haka zalika shugaban APC na kasa, Farfesa Yilwatda Nentawe ya ce nan gaba babu wanda za a ba mukami a gwamnatinsu sai wanda yake da rajistar jam'iyyar APC.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

