Abokin Takarar Kwankwaso Ya Fito Ya Yi Magana ana Batun Shirin Abba na Komawa APC

Abokin Takarar Kwankwaso Ya Fito Ya Yi Magana ana Batun Shirin Abba na Komawa APC

  • Dan takarar mataimakin shugaban kasa a inuwar NNPP a zaben 2025, Bishof Isaac Idahosa ya jaddada goyon bayansa ga Kwankwaso
  • Babban limamim cocin ya bayyana Dr. Rabiu Kwankwaso a matsayin jagora amintacce, wanda ke tsayawa talakawan da aka yi watsi da su
  • Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake zargin alaka ta yi tsami tsakanin jagoran NNPP da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Manyan jiga-jigan NNPP na ci gaba da bayyana ra'ayoyinsu game da dambarwar da ke faruwa musamman bayan bullar rade-radin Gwamna Abba Kabir Yusuf zai koma APC.

Duk da har yanzu, gwamnan na jihar Kano bai fito ya yi magana da bakinsa ba amma jita-jitar na ci gaba da kara karfi, kuma alamu na nuna alaka ta yi tsami tsakaninsa da Kwankwaso.

Kara karanta wannan

Mataimakin gwamnan Kano ya dawo, ya nuna wanda zai bi tsakanin Abba da Kwankwaso

Idahosa.
Abokin takarar Kwankwaso a zaben shugaban kasa na 2023, Bishof Isaac Idahosa Hoto: Bishop Isaac Idahosa
Source: Facebook

Leadership ta rahoto cewa, dan takarar mataimakin shugaban kasa a inuwar NNPP a zaben 2023 kuma babban limamin coci a Najeriya, Bishof Isaac Idahosa ya fito ya yabi Kwankwaso a wannan lokaci.

Bishof Idahosa ya goyi bayan Kwankwaso

Limamin cocin, wanda shi ne abokin takarar Kwankwaso a zaben 2023, ya bayyana madugun Kwankwasiyya a matsayin jagora mai kaunar talakawa.

Bishof Idahosa, ya bayyana cewa akwai wani babban aiki na kasa da ke jiran sa, yayin da ya sake jaddada goyon bayansa ga jagorancin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

A cikin wata sanarwa da ya fitar jiya Laraba, Idahosa ya kwatanta Kwankwaso da matsayin jagora amintacce wanda ya sadaukar da rayuwarsa domin jin dadin talakawan Jihar Kano da ma Najeriya baki daya.

Idahosa ya yaba da nagartar Kwankwaso

A rahoton Vanguard, Idahosa ya bayyana cewa:

"Kwankwaso gwarzon kasa ne wanda a kowane lokaci yake nuna damuwarsa ga gajiyayyu. Jagora ne abin dogaro wanda ko da yaushe yake tsayawa tsayin daka ga talakawan da aka maida saniyar ware.

Kara karanta wannan

An zo wajen: Kwankwaso ya kafa sharadin sauya sheka zuwa jam'iyyar APC

"Kuma ni dai na yi amannar cewa yana daya daga cikin mutanen da za su iya ciyar da Najeriya gaba."
Isaac Idahosa da Kwankwaso.
Jagoran NNPP, Rabiu Kwankwaso tare da abokin takararsa a zaben 2023, Bishof Isaac Idahosa Hoto: Bishop Isaac Idahosa
Source: Facebook

Limamin coci ya ba mambobin NNPP shawara

Malamin cocin ya yi kira ga mambobin jam’iyyar NNPP a fadin kasar nan da su hada kai su mara wa Kwankwaso baya, inda ya kara cewa:

"Hidimar kasa ne ke kiran Kwankwaso. Ya riga ya biya bashin da talakawa ke binsa, kuma nan ba da jimawa ba za a ji wata babbar sanarwa a matsayin sakamakon ayyukan kwarai da ya shuka," in ji shi.

Ya kammala da kira ga mambobin NNPP da su kara kaimi wajen goyon bayan manufofin Kwankwaso, yana mai cewa kishin kasa da hangen nesa irin nasa ne kadai zai fitar da Najeriya daga halin da take ciki.

Mataimakin gwamna ya bi Kwankwaso

A baya, kun ji cewa an hangi mataimakin gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo a gidan jagoran NNPP na kasa, Dr. Rabiu Kwankwaso.

Aminu Gwarzo ya nuna alamun bangaren da ya dauka ne a daidai lokacin da rade-radin ficewar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jam’iyyar APC ke kara karfi.

Mataimakin gwamnan na daya daga cikin manyan na kusa da Kwankwaso, wadanda ake hasashen za su iya ci gaba da zama a NNPP maimakon tafiya APC tare da Abba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262