'Yan Adawa Sun Tashi Tsaye, PDP Za Ta Gana da Manyan Jagororin ADC, Atiku da Peter Obi

'Yan Adawa Sun Tashi Tsaye, PDP Za Ta Gana da Manyan Jagororin ADC, Atiku da Peter Obi

  • Jam'iyyar PDP za ta gana da manyan jagororin hadaka, Peter Obi da Atiku Abubakar yayin da shirye-shiryen 2027 ke kara kankama
  • Shugaban PDP na yankin Kudu maso Kudu, Emmanuel Ogidi ya ce hakan wani bangare ne na kokarin sake gina tsagin adawa
  • PDP mai hamayya na ci gaba da fuskantar rigingimun cikin gida tun bayan zaben 2023, wanda ya kai ga darewarta zuwa gida biyu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Babbar jam'iyyar adawa ta fara shirya yadda za ta gana da tsohon 'dan takarar shugaban kasa na LP, Peter Obi da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar.

Jigon PDP, Emmanuel Ogidi ya ce za a yi wannan ganawa tsakanin jam'iyyar da Atiku, Obi da wasu manyan jagororin adawa domin sake gina babbar jam'iyyar adawa a Najeriya.

Kara karanta wannan

APC ta bugi kirji, ta fadi adadin kuri'un da Tinubu zai samu a Filato a 2027

Peter Obi da Atiku.
Tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar Hoto: @PeterObi, Atiku Abubakar
Source: Facebook

Ogidi, wanda shi ne shugaban PDP na yankin Kudu maso Kudu, ya bayyana hakan ne a shirin The Morning Brief na gidan talabijin na Channels TV a ranar Laraba.

Jam'iyyar PDP ta fara tuntubar tsofaffin shugabanni

Ya ce PDP ta fara tattaunawa da shugabanni da manyan mutane masu tasiri a ƙasar nan, inda tuni ta gana da tsofaffin shugabannin ƙasa biyu, Olusegun Obasanjo da Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB).

“Mun riga mun gana da tsohon Shugaban Ƙasa Obasanjo da kuma IBB. Wannan duka wani ɓangare ne na nuna wa ’yan Najeriya cewa PDP na nan da ranta kuma tana ci gaba da motsi.
"Na san za ku tambaye ni batun Peter Obi; Eh, shi ma muna da shirin ganawa da shi,” in ji Ogidi.

PDP na shirin ganawa da Atiku da Obi

Ya ƙara da cewa PDP za ta kuma gana da Atiku Abubakar, yana mai cewa jam’iyyar ita ce ainihin fuskar dimokuraɗiyya a Najeriya.

Kara karanta wannan

Rikicin PDP: An ji abin da Jonathan ya fadawa shugabannin jam'iyyar a Abuja

Peter Obi da Atiku Abubakar dai tsofaffin ’yan PDP ne, inda a shekarar 2019 Obi ya yi takarar mataimakin shugaban ƙasa, yayin da Atiku yake matsayin 'dan takarar shugaban ƙasa.

Atiku kuma shi ne ɗan takarar PDP a zaɓen 2023, daga bisani, su biyun suka koma jam’iyyar ADC, dandalin hadakar manyan 'yan adawa a kasar nan.

Shugaban PDP na kasa, Tanimu Turaki.
Shugaban jam'iyyar PDP na kasa, Taninu Turaki Hoto: PDP Nigeria
Source: Facebook

A ranar Talata kuma, mambobin Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na PDP sun gana da tsohon Shugaban Ƙasa, Dr. Goodluck Jonathan a ofishinsa da ke Maitama, Abuja.

Taron ya samu jagorancin shugaban jam’iyyar na ƙasa, Tanimu Turaki, tare da sauran manyan ’yan jam’iyyar, kamar yadda Vanguard ta rahoto.

A halin yanzu, bangarori biyu na iƙirarin shugabancin PDP a matakin ƙasa, biyo bayan taron jam’iyyar da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo.

Abin da Jonathan ya fadawa PDP

A wani labarin, kun ji cewa shugaban PDP na kasa, Tanimu Turaki (SAN) ya shaida wa manema labarai cewa sun je wurin Jonathan domin gabatar masa da sabon kwamitin NWC na kasa.

Ya ce tsohon Shugaba Jonathan ya tabbatar masu da cewa har yanzu shi cikakken mamba ne mai katin PDP, kuma zai ci gaba da kasancewa mai bada gudummuwa a jam’iyyar.

Turaki ya ce maganganun Jonathan sun ƙarfafa gwiwar jam’iyyar, tare da ba su kwarin gwiwa kan makomar PDP a siyasance.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262