Gwamna Abdulrazaq Ya Gano Jam'iyyar da Ta Dace da Mulkin Najeriya

Gwamna Abdulrazaq Ya Gano Jam'iyyar da Ta Dace da Mulkin Najeriya

  • Mai girma Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya yi tsokaci kan jam'iyyar da ta dace da mulkin Najeriya
  • Shugaban na kungiyar gwamnonin Najeriya ya bayyana cewa jam'iyyar APC ita ce mafi dacewa da jan ragamar al'amuran Najeriya
  • Gwamna Abdulrazaq ya nuna cewa APC ce kadai jam'iyyar da ta kawo ci gaba a matakin kasa, jihohi da kananan hukumomi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Kwara - Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana cewa jam’iyyar APC ita ce jam’iyya mafi dacewa da tafiyar da al’amuran Najeriya.

Gwamna Abdulrazaq ya bayyana APC a matsayin wata babbar kungiyar siyasa ta musamman, wadda ake ganin ita ce jam’iyya mafi girma a Afirka baki ɗaya.

Gwamna Abdulrahman ya yabi jam'iyyar APC
Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq na jihar Kwara Hoto: Abdulrahman Abdulrazaq
Source: Facebook

Jaridar The Nation ta ce gwamnan ya yi wannan jawabi ne yayin kaddamar da taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki na APC a jihar, tare da fara rajistar yanar gizo da tantance mambobin jam’iyyar.

Kara karanta wannan

Ana batun sauya shekar Gwamna Abba, Kwankwaso ya aika sako ga masu raina NNPP

Gwamna Abdulrazaq ya yi rajistar APC

Gwamna AbdulRazaq, wanda aka rubuta sunansa a matsayin mutum na farko da ya yi rajista a jam’iyyar a Kwara, ya ce an shirya wannan aikin ne domin Karfafa APC tare da samun sahihin adadin mambobinta don kyakkyawan shiri da tsari.

Ya ce duk wanda ke da sha’awar shiga jam’iyyar ya kamata a ba shi dama, yana mai gargadin cewa kada a ware ko a hana kowa shiga rajistar.

Gwamnan ya kuma sanar da cewa duk masu niyyar tsayawa takarar kujerun siyasa a 2027 za su samu dama iri daya, ba tare da nuna wariya ba.

Gwamna ya ba masu neman takara shawara

Abdulrahman Abdulrazaq wanda kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya (NGF), ya shawarci duk masu neman yin takara a jihar da su nemi goyon bayan mambobin jam’iyyar tare da jawo sababbin mambobi, jaridar Vanguard ta kawo labarin.

“Yana da matuƙar muhimmanci mu san adadin mambobin wannan kungiya ta musamman (APC), wadda ake ganin ita ce jam’iyya mafi girma a Afirka."

Kara karanta wannan

An dakatar da shugaban jam'iyyar PDP da aka gano yana biyayya ga ministan Abuja

"Ita ce kaɗai jam’iyyar da ta bunkasa Najeriya da dukkan jihohinta, har ma da kananan hukumomi."

- Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq

Jiga-jigan jam'iyyar APC sun halarci taro

Manyan jiga-jigan jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar sun halarci taron masu ruwa da tsaki da kuma kaddamar da aikin rajistar da sake tantance mambobin APC.

“Muna son sanin adadinmu domin mu iya tsara tsare-tsare, neman goyon baya, da kare kanmu yadda ya kamata, tare da karfafa kanmu ba tare da barin kowa a baya ba."
“Ga waɗanda aka ɗora wa wannan aiki, kada ku hana kowa. Muna bukatar dukkan mambobin da za mu iya samu. Ku tabbatar kun yi rajistar ba mambobinmu kaɗai ba, har da neman sababbin mambobi."
“Wannan dama ce ta jawo sababbin mambobi. Kun ga ayyukan da aka yi daga matakin tarayya zuwa jiha da kananan hukumomi. Ku yi amfani da su wajen tallata jam’iyyar domin mu faɗaɗa ta fiye da inda muke a baya.”

- Gwamna Abdulrahman AbdulRazaq

Gwamna Abdulrazaq ya ba 'yan APC shawara
Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq na jawabi a wajen taro Hoto: Abdulrahman Abdulrazaq
Source: Facebook

Gwamna Abdulrazaq ya ce gwamnatinsa ta aiwatar da ayyuka masu yawa a dukkan fannoni, wanda hakan ya sa jihar Kwara ta samu ci gaba fiye da kowane lokaci a tarihinta.

Kara karanta wannan

APC ta manta da rawar da Wike ya taka, ta fadi jagoran jam'iyyar a Rivers

PDP ta soki Gwamna Abdulrazaq

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar PDP mai adawa a Kwara ta caccaki Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq.

Jam'iyyar PDP mai hamayya a jihar da Najeriya ta soki Gwamna Abdulrazaq kan rashin mayar da martani bayan fashewar da ta auku a Offa.

Hakazalika, jam'iyyar PDP ta ce shiru da gwamnatin ta yi ya bar mazauna Offa cikin damuwa, tsoro da neman karin bayani kan abin da ya faru.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng