Babbar Magana: An Fara Neman a Tsige Bola Tinubu daga Kujerar Shugaban Kasa

Babbar Magana: An Fara Neman a Tsige Bola Tinubu daga Kujerar Shugaban Kasa

  • Jam'iyyar PRP ta nuna damuwa kan zargin da ake na sauya wasu sassan dokokin haraji bayan majalisar tarayya ta amince da su
  • Tuni dai Majalisa ta kafa kwamitin wucin gadi da zai gudanar da bincike kan banbanci tsakanin dokokin da ta amince da su da wadanda ke hannun gwamnati
  • PRP ta bayyana cewa matukar aka samu Shugaba Bola Ahmed Tinubu da hannu a wannan aikin, tana kira da a tsiga shi nan take

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Dambarwar canza dokokin sake fasalin haraji a Najeriya na ci gaba da daukar hankali yayin da jam'iyyun siyasa suka fara bayyana matsayarsu.

Jam’iyyar PRP ta yi kira da a tsige Shugaba Bola Ahmed Tinubu daga mukaminsa idan aka tabbatar da cewa yana da hannu a murɗawa ko sauya dokokin haraji da Majalisa ta amince da su.

Kara karanta wannan

Kasar Amurka ta yanke matsaya game da maganar turo dakarun sojoji Najeriya

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnati da ke Abuja Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Jam’iyyar ta yi Allah-wadai da abin da ta kira sakaci da ƙa’idojin mulki da kuma nuna halin ko-in-kula kan kundin tsarin mulki da gwamnatin tarayya ke yi, in ji rahoton Leadership.

Majalisa ta fara daukar mataki

Idan baku manta ba Majalisar Wakilai ta kafa kwamitin bincike na mutum bakwai domin bincikar zargin da ake yi na sauya dokokin haraji da ta amince da u.

Ana sa ran kwamitin zai gudanar da bincike mai zurfi don gano bambancin da ke tsakanin dokokin haraji da Majalisa ta amince da su da kuma idokokin da aka wallafa a jaridar gwamnati.

Da take mayar da martani, jam’iyyar PRP ta ce idan aka samu hujjojin da ke nuna cewa Shugaba Tinubu yana da hannu a wannan zargi, to ya dace a tsige shi nan take.

A cikin wata sanarwa da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Falalu Bello, ya fitar, PRP ta bayyana cewa babu wanda ya fi iarfin doka, har shi kansa shugaban kasa.

Kara karanta wannan

zarge zargen rashawa: Cikakken jerin sunayen ministocin Buhari da EFCC ta cafke

PRP ta fadi sharadin tsige Tinubu

Ta ce lamarin na nuna cewa bangaren zartarwa na gwamnati ya riƙa sauya dokoki a ɓoye bayan Majalisa ta amince da su, ba tare da sahalewar ‘yan majalisa ba, in ji Daily Trust.

“Wannan aiki na rashin gaskiya daga bangaren zartarwa, wanda ya haɗa da ƙara wasu sassa, cire wasu, ko sauya muhimman tanade-tanade bayan doka ta riga ta samu amincewar Majalisa, na nuna raini ga tsarin mulki.
"Idan aka samu hujjojin da ke nuna Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana da hannu a wannan laifi, PRP na kira da a tsige shi daga mukaminsa ba tare da ɓata lokaci ba domin shugaban ƙasa bai fi karfin doka ba,” in ji jam’iyyar.
Zauren Majalisar Wakilai.
Mambobin Majalisar Wakilan Tarayya a lokacin da suke zama a Abuja Hoto: @HouseNGR
Source: Facebook

Shugaba Tinubu ya gamu da koma baya

A wani labarin, kun ji cewa wata kungiyar magoya bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, mai suna Tinubu Vanguard ta dawo daga rakiyarsa.

Kungiyar, wacce ke da dubban mambobi a jihohin Arewa 19 da Abuja ta bayyana cewa ta janye goyon bayan da take wa Shugaba Bola Tinubu saboda an yi watsi da ita.

Kungiyar ta kuma janye goyon bayanta ga jam’iyyar APC mai mulki, bisa dalilan watsi da ita, rashin karramawa da kuma wahalhalun da mambobinta ke fuskanta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262