Cikakken Jerin Gwamnonin Najeriya da Jam'iyyunsu a Watan Disamban 2025

Cikakken Jerin Gwamnonin Najeriya da Jam'iyyunsu a Watan Disamban 2025

  1. Jam’iyyar APC ta kara tabbatar da cikakken ikonta a yawancin jihohin Najeriya, inda take rike da kujerun gwamnoni 27 a faɗin yankuna daban-daban na kasar
  2. Jam’iyyun adawa sun ci gaba da kasancewa da karamin tasiri amma mai muhimmanci, inda PDP ke mulkin jihohi biyar, yayin da wasu jam’iyyu ke da guda uku
  3. Rarrabuwar gwamnonin ya nuna banbancin ra'ayin siyasa, domin kuwa har yanzu akwai jihohin da ke karkashin kananan jam'iyyu irinsu LP, APGA da NNPP

​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Abuja, FCT - Yanayin siyasar Najeriya zuwa tsakiyar watan Disamba na shekarar 2025 ya nuna karkata sosai ga jam’iyyar APC mai mulki, wadda ke rike da mafi yawan gwamnatocin jihohi a faɗin kasar.

Rarraba gwamnonin bisa jam’iyya ya nuna yadda sakamakon zaɓuɓɓukan baya-bayan nan da kuma sauye-sauyen kawancen siyasa a matakin jihohi suka kasance.

Kara karanta wannan

Shugaban Ƙasa, gwamnoni da ciyamomi sun raba Naira tiriliyan 1.92 a watan Nuwamba

Gwamnonin Najeriya da jam'iyyun da suke ciki
Wasu gwamnonin Najeriya tare da Shugaba Bola Ahmed Tinubu Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Jam'iyyar APC na da mafi yawan gwamnoni

Wani amfani da shafin X mai suna @ImranMuhdz, ya sanya cikakken jerin gwamnonin Najeriya da jam'iyyun da suka fito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Da gwamnoni 27, APC ta kasance jam’iyya mafi karfi kuma mafi yawan gwamnoni a cikin jihohi 36 na Najeriya.

Ikon APC ya shafi muhimman cibiyoyin tattalin arziki da kuma jihohi masu muhimmancin siyasa, ciki har da Legas, Ribas, Delta da Kaduna.

Wannan faɗaɗɗen tasiri ya sanya jam’iyyar a matsayi mai karfi gabanin zaɓuka masu zuwa da kuma tattaunawar mulki tsakanin gwamnatin tarayya da jihohi.

Jam'iyyar APC ta kasance da mafi yawan gwamnoni tun bayan zaben shekarar 2023 da aka gudanar a cikin jihohi 28 na Najeriya.

Hakazalika, jam'iyyar APC ta yi nasara a wasu zabubbukan gwamnoni da aka gudanar a jihohin Kogi da Edo.

Daga baya wasu daga cikin gwamnonin jam'iyyun adawa sun rika yin tururuwa zuwa jam'iyyar APC mai mulki.

Kara karanta wannan

Gwamna Aiyedatiwa ya fadi dalilin da ya sa gwamnonin PDP ke komawa APC

Jam'iyyun adawa na da tsirarun gwamnoni

Jam’iyyar PDP ta biyo baya a matsayi na biyu, inda take da gwamnoni a ƴan jihohi kaɗan na Najeriya.

Jaridar The Punch ta ce ya zuwa watan Disamban 2025, gwamnoni shida suka rage a cikin jam'iyyar PDP, wannan adadin ya ragu zuwa biyar biyo bayan sauya shekar da gwamnan Taraba, Agbu Kefas, ya yi zuwa APC.

Tun bayan zaben shekarar 2023, gwamnoni shida ne suka fice daga jam'iyyar PDP, inda biyar daga cikinsu suka koma APC, yayin da daya kuma ya koma jam'iyyar Accord Party.

Duk da cewa PDP ta ci gaba da kasancewa mai tasiri a wasu sassan Arewa Maso Gabas, Arewa Ta Tsakiya da Kudu Maso Yamma, raguwar yawan jihohin da take mulki na nuna kalubalen da take fuskanta wajen dawo da ƙarfinta tun bayan zaɓukan gama-gari na karshe.

Jam'iyyun siyasa na da gwamnoni a Najeriya
Shugaba Bola Tinubu tare da wasu gwamnonin jihohin Najeriya Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

A kasa akwai cikakken jerin gwamnonin Najeriya bisa jam’iyyun siyasa zuwa ranar 17 ga watan Disamba, 2025.

Kara karanta wannan

APC: Atiku da manyan 'yan adawa sun taso Tinubu a gaba game da mamaye Najeriya

Jam'iyyar APC - Gwamnoni 27

  1. Jihar Akwa Ibom: Umo Eno
  2. Jihar Bayelsa: Douye Diri
  3. Jihar Benue: Hyacinth Alia
  4. Jihar Borno: Babagana Umara Zulum
  5. Jihar Cross River: Bassey Otu
  6. Jihar Delta: Sheriff Oborevwori
  7. Jihar Ebonyi: Francis Nwifuru
  8. Jihar Edo: Monday Okpebholo
  9. Jihar Ekiti: Biodun Oyebanji
  10. Jihar Enugu: Peter Mbah
  11. Jihar Gombe: Muhammad Inuwa Yahaya
  12. Jihar Imo: Hope Uzodimma
  13. Jihar Jigawa: Umar Namadi
  14. Jihar Kaduna: Uba Sani
  15. Jihar Katsina: Dikko Umar Radda
  16. Jihar Kebbi: Nasir Idris
  17. Jihar Kogi: Usman Ododo
  18. Jihar Kwara: Abdulrahman Abdulrazaq
  19. Jihar Legas: Babajide Sanwo-Olu
  20. Jihar Nasarawa: Abdullahi Sule
  21. Jihar Neja: Mohammed Umar Bago
  22. Jihar Ogun: Dapo Abiodun
  23. Jihar Ondo: Lucky Aiyedatiwa
  24. Jihar Rivers: Siminalayi Fubara
  25. Jihar Sokoto: Ahmad Aliyu
  26. Jihar Taraba: Agbu Kefas
  27. Jihar Yobe: Mai Mala Buni

Jam'iyyar PDP - Gwamnoni 5

  1. Jihar Adamawa: Ahmadu Umaru Fintiri
  2. Jihar Bauchi: Bala Mohammed
  3. Jihar Oyo: Seyi Makinde
  4. Jihar Plateau: Caleb Mutfwang
  5. Jihar Zamfara: Dauda Lawal

Jam'iyyar Accord Party - Gwamna 1

Kara karanta wannan

Gwamna Bago ya goyi bayan wa'adi 1 a mulki, ya fadi amfaninsa

1. Jihar Osun: Ademola Adeleke

Jam'iyyar Labour Party (LP) - Gwamna 1

1. Jihar Abia: Alex Otti

Jam'iyyar APGA - Gwamna 1

1. Jihar Anambra: Charles Chukwuma Soludo

Natasha ta magantu kan shiga jam'iyyar APC

A wani labarin kuma, kun ji cewa Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a majalisar dattawa, Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi magana kan shiga jam'iyyar APC.

A yayin wata hira da aka yi da ita, Sanata Natasha ta ce ba za ta taba komawa APC ba saboda wasu dalila nata na karan kanta.

Sanatar ta ce har yanzu akwai wasu daga fadar shugaban kasa da ke ci gaba da yi mata tayin ta dawo jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng