"Sun Yi Kadan": Wike Ya Ware Gwamnoni 2 Ya Yi Musu Saukale kan Rikicin PDP

"Sun Yi Kadan": Wike Ya Ware Gwamnoni 2 Ya Yi Musu Saukale kan Rikicin PDP

  • Jam'iyyar PDP na ci gaba da fama da rikicin cikin gida da ya dade yana addabarta, wanda hakan ya sanya ta dare gida biyu
  • Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya cika baki da cewa babu wanda ya isa ya kore shi daga jam'iyyar PDP
  • Wike ya bayyana cewa ya dade a cikin PDP kuma wadanda ke kokarin raba shi da ita sun yi kadan domin ba zai yarda da hakan ba

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ba a isa a kore shi daga jam'iyyar PDP ba.

Wike ya bayyana cewa ba za a kore shi daga PDP ba, musamman ma daga mutanen da suka shiga jam’iyyar bayan shi.

Wike ya ragargaji Gwamna Bala Mohammed
Nyesom Wike tare da Gwamna Bala Mohammed na Bauchi Hoto: @GovWike, @SenBalaMohammed
Source: Twitter

Jaridar The Cable ta ce Wike ya yi wannan jawabin ne a ranar Lahadi yayin wani zaman NEC na ɓangaren jam’iyyar PDP da yake jagoranta, wanda aka gudanar a gidansa da ke Abuja.

Kara karanta wannan

Tsohon kakakin PDP na kasa ya bi sahun gwamnoni 5, ya fice daga jam'iyyar

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce Gwamna Bala Mohammed na Bauchi da Gwamna Seyi Makinde na Oyo sun shiga PDP lokacin da ya riga ya dade a cikinta.

Jam'iyyar PDP na fama da rikice-rikice

A watan da ya gabata, ɓangaren PDP da Makinde da Bala ke mara wa baya ya kori Wike da magoya bayansa, ciki har da tsohon gwamnan Ekiti, Ayodele Fayose da tsohon sakatare jam'iyyar na kasa Samuel Anyanwu.

Sauran sun hada da tsohon sakataren tsare-tsare, Umar Bature, tsohon lauyan jam'iyya, Kamaldeen Ajibade da wasu shugabanni daga jihohi daban-daban.

Tun daga lokacin, ɓangaren Wike ya kafa sabon kwamitin gudanarwa na kasa (NWC), BoT da NEC.

Nyesom Wike ya dauki zafi kan rikicin PDP

Wike ya bayyana cewa ya kasance cikin PDP tun daga lokacin da aka fara shirin kafa ta a shekarar 1990, inda ya kara da cewa babu wanda ya isa ya kori mutanen da suka yi wa jam'iyyar hidima, za a samu rahoton a jaridar Vanguard.

Kara karanta wannan

Yadda Yerima ya yi aure da abubuwan da suka faru bayan rigima da Wike

“Ta yaya mutanen da suka same ni a gidana za su kore ni? Ba zan taba bari hakan ta faru ba."
“Ku tambayi Bala Mohammed wace jam'iyya ya yi takarar sanata. Jam'iyyar mu ta ba mutane da dama mafaka inda suka zama sanatoci da gwamnoni."
“Amma yanzu suna tunanin za su iya korar mutanen da suka yi sadaukarwa ga jam'iyyar tun kafuwarta. Idan an bar su sun yi hakan a baya, mu ba za mu kyale su ba."

- Nyesom Wike

Wike ya yi maganganu kan rikicin jam'iyyar PDP
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike Hoto: @GovWike
Source: Facebook

Wike ya caccaki gwamnonin PDP

Wike ya caccaki bangaren Kabiru Tanimu Turaki wanda Gwamna Bala da Seyi Makinde ke marawa baya, kan bin umarnin kotu tare da gudanar da haramtaccen babban taro.

"Kun yi babban taro ba tare da bin umarnin kotu ba, yanzu kuma kuna neman babbar kotun tarayya ta amince da ku. Idan har INEC ta amince da ku, me yasa kuka sake komawa kotu."

- Nyesom Wike

Ministan ya yi gargadin cewa hakan zai iya gurbata PDP, inda ya nuna cewa dole ne shugabanni su tashi tsaye domin kare jam'iyyar wadda aka kafa a shekarar 1998.

Kara karanta wannan

Da gaske an kama Wike a Faransa? Ministan ya fadi halin da yake ciki

Wike ya kori shugaban hukumar FCT-IRS

A wani labarin kuma, kun ji cewa ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya yi garambawul a hukumar tattara harajin FCT watau (FCT-IRS).

Nyesom Wike ya tsige shugaban rikon kwarya na hukumar tattara Haraji ta FCT (FCT-IRS), Michael Ango, daga mukaminsa nan take.

Ministan na Abuja ya umarci jami’i mafi girma a FCT-IRS da ya gaggauta karɓar jagoranci domin ci gaba da gudanar da ayyukan hukumar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng