El Rufai Ya Hango Makomar Gwamnonin da Ke Komawa APC a Zaben 2027

El Rufai Ya Hango Makomar Gwamnonin da Ke Komawa APC a Zaben 2027

  • Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya yi tsokaci kan babban zaben shekarar 2027 da ake tunkara
  • Nasir El-Rufai ya bayyana cewa sauya shekar da wasu gwamnoni ke yi APC, ba za ta hana 'yan Najeriya zaben shugabannin da suke so ba
  • Tsohon gwamnan ya kuma yi kira ga 'yan Najeriya da su shiga jam'iyyar ADC domin ceto kasar nan daga halin da ta tsinci kanta a ciki

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Plateau - Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya yi magana kan yawan sauya shekar da wasu gwamnoni ke yi zuwa jam'iyyar APC.

Malam Nasir El-Rufai ya ce yawan sauya shekar da gwamnonin ke yi, ba zai hana ’yan Najeriya zabar shugabannin da suke so a zaben 2027 ba.

El-Rufai ya ce 'yan Najeriya na komawa jam'iyyar ADC
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai Hoto: @elrufai
Source: Twitter

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa jigon na jam’iyyar ADC ya bayyana hakan a yayin bude ofishin tuntuɓa da wayar da kai na ADC na kasa da aka yi a Jos, ranar Laraba.

Kara karanta wannan

Abu ya kacame, sabon shugaban PDP da tsagin Wike na iya arangama a taro

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me El-Rufai ya ce kan masu sauya sheka?

Ya ce yayin da gwamnonin jam’iyyar PDP ke komawa APC, ’yan Najeriya kuwa suna komawa ADC.

El-Rufa’i ya bayyana cewa ADC na da cikakkiyar damar hada kan al’ummar Plateau idan ta karɓi jagorancin jihar da ma Najeriya baki daya a 2027.

Tsohon gwamnan ya ce komai bai tafiya daidai a halin yanzu, amma har yanzu akwai fata.

Ya yi kira ga mazauna jihar su mara wa ADC baya domin ta samu damar karɓar mulki a jihar da kuma kasa baki ɗaya.

“Shekaru 40 da suka gabata ina zuwa Plateau kusan kowane mako saboda wacce zan aura a lokacin tana yin NYSC a Jos. Har bayan aure muna ziyartar Jos a karshen mako. Amma daga lokacin abubuwa sun lalace a Jos, Plateau.”
“Ina fatan idan aka samu kyakkyawan shugabanci a jiha da kasa, za mu iya hada kan al’ummar Plateau daga kowace kabila da addini, domin jihar ta koma wurin zaman lafiya da yawon bude ido kamar yadda muka sani. Muna rokon Allah Ya ba mu ikon hada kan ku.”

Kara karanta wannan

Rikicin PDP: Sanata Anyanwu ya dora laifin abubuwan da ke faruwa kan gwamnoni 7

- Nasir El-Rufai

'Yan Najeriya za su kada gwamnoni

Ya ce ’yan Najeriya ba sa jin daɗin jagorancin PDP da APC, don haka suna neman sabon shugabanci, yana mai cewa da goyon bayan jama’a ADC za ta kayar da APC mai mulki a babban zabe na gaba.

“Na san kowa ya gaji da gwamnatin APC da PDP a fadin kasa. Kowa ya jingina da ADC domin ta ceci Najeriya. Gwamnonin PDP na komawa APC amma ’yan Najeriya na komawa ADC. Da ikon Allah, ’yan Najeriya miliyan 230 za su kayar da gwamnoni 25.”
“’Yan Najeriya sun yanke shawarar cewa a 2027 za su zabi ADC. Abin da ya rage shi ne mu hada kai mu tara ’yan jam’iyya gaba daya, mu fito da kyawawan ’yan takara da manufofi masu amfani ga ’yan kasa.”

- Nasir El-Rufai

El-Rufai ya ce 'yan Najeriya za su zabi wanda suke so a 2027
Babban jigo a jam'iyyar ADC, Nasir El-Rufai Hoto: @elrufai
Source: Twitter

El-Rufai ya ja hankalin matasa

El-Rufa’i ya kara jan hankalin matasa da mata, inda ya bayyana cewa:

Kara karanta wannan

Sauya sheka: Sanata Ndume ya hango matsalar da za ta samu jam'iyyar APC

“Kowane mutum a nan na da rawar da zai taka. ADC ita ce jam’iyyar kadai da ta ware kashi 40 na mukaman jagoranci ga matasa, da kashi 35 ga mata masu neman mukami. Jam’iyya ce ta matasa da mata.”

Tsohon shugaban PDP ya koma ADC

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon shugaban PDP a jihar Kwara, ya yi murabus daga ci gaba da zama mamba a jam'iyyar.

Hon. Babatunde Mohammed ya raba gari da jam'iyyar PDP mai adawa ne bayan kwashe fiye da shekara 20 a cikinta.

Hakazalika, tsohon shugaban na PDP wanda ya kuma taba zama shugaban majalisar dokokin jihar, ya sanar da komawarsa zuwa jam'iyyar ADC.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng