'Dan Ganduje Ya Yi Ruwan Kayan Arziki a Kano, 'Yan Kwankwasiyya 500 Sun Koma APC
- Sama da mutane 3,000 ne suka ci gajiyar shirin tallafin da Umar Abdullahi Ganduje, dan tsohon shugaban APC ya kirkiro a Kano
- Umar ya raba kayayyaki da suka hada da Keke Napep da kayan noma na zamani domin taimaka wa mutane su dogara da kansu
- Bayan haka, tsohon 'dan takarar majalisar wakilan tarayyar ya kuma karbi mambobin NNPP 500 da suka sauya sheka zuwa APC
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Ɗan tsohon shugaban APC, kuma Babban Daraktan Sashen Fasaha na Hukumar Bunkasa Wutar Lantarki a Karkara ta Kasa (REA), Umar Abdullahi Ganduje, ya tallafawa magoya baya sama da 3,000 a jihar Kano.
Umar, ɗan tsohon gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya kaddamar da mataki na farko na shirin tallafin ne a wurin taron da aka gudanar a Armani, Kano, a daren Lahadi.

Source: Facebook
The Nation ta tattaro cewa hakan na kunshe ne a wata sanarwa da Kakakin Tsohon Shugaban APC, Edwin Olofu, ya fitar a Abuja ranar Litinin.
Umar Ganduje ya tallafawa 'yan Kano
Kayan tallafin da aka raba wa matasa daga duka kananan hukumomi 44 sun haɗa da kayan noma da sauran kayan bunƙasa aikin gona domin taimaka wa mutane su dogara da kai.
Umar ya ce wannan tallafi “kadan ne daga abin da ya shirya” domin akwai manyan shirye-shiryen tallafi da ya tanada musamman ga matasa da mata a fadin jihar Kano.
Umar da aka fi sani da Abba Ganduje ya bayyana cewa burinsa na taimakon jama’a ne ya sa ya kirkiro shirin, ba wai ga mutanen mazabarsa ta Tofa/Dawakin-Tofa/Rimingado kaɗai ba, har ma ga al'ummar Kano baki daya.
Kayan da Abba Ganduje ya raba a Kano
'Dan siyasar ya kuma bayyana cewa za a ƙaddamar da zagaye na biyu na shirin nan ba da jimawa ba.
A sanarwar da ya wallafa a Facebook, Umar ya ce:
“Mun riga mun fara shirye-shiryen mataki na gaba na wannan tallafi, wannan ba shi ne na karshe ba, duk wani ɗan APC da bai samu a yau ba, kada ya damu, lokaci zai zo,” in ji shi.
Kayan da aka raba sun haɗa da, Keke Napep, kananan motocin dako, takin zamani, magungunan kashe ciyawa, ingantattu iri, na’urorin sola, injin ban ruwa da sauransu.

Source: Facebook
'Yan NNPP 500 sun koma APC
Bayan rabon kayan, Umar Ganduje ya karɓi mutum 500 daga jam’iyyar NNPP da suka koma APC.
Ya tabbatar masu da cewa jam’iyyar APC za ta karɓe su hannu bibbiyu ba tare da nuna masu wariya ba.
“Mun yaba da jarumtarku ta gano gaskiya da shiga APC, jam’iyya mafi ƙarfi a Afrika,” in ji shi.
Shugaban APC ya nemi afuwa a Kano
A wani rahoton, kun ji cewa shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Abdullahi Abbas, ya nemi afuwar mazauna Fagge bayan kalamansa sun haifar da ce-ce-ku-ce.
Rahotanni sun ce kalaman Abdullahi Abbas sun harzuka wasu daga cikin shugabannin al'umma a Fagge, kuma har sun kai kara gaban kotu.
Sai dai duk da haka, Abbas ya jaddada cewa al'ummar karamar hukumar Fagge ba su fahimci abin yake nufi ba, amma ya na rokon gafararsu kan kalaman da ya fadi
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


