PDP na Dab da Rasa Taraba, Gwamna Ya Bayyana Ranar da Zai Sauya Sheka zuwa APC

PDP na Dab da Rasa Taraba, Gwamna Ya Bayyana Ranar da Zai Sauya Sheka zuwa APC

  • Bayan tsawon lokacin ana magana kan sauya shekarsa, Gwamna Agbu Kefas ya tabbatar da cewa zai koma APC a makon gobe
  • Gwamna Kefas ya bayyana cewa zai sauya sheka daga PDP zuwa APC mai mulki a hukumance ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamba, 2027
  • Majalisar zartarwa ta Taraba ta nuna goyon baya ga gwamnan, ta ce wannan ba tafiya ce da ta shafi duka al'ummar jihar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Taraba, Nigeria - Gwamna Agbu Kefas na jihar Taraba ya kammala duk wasu shirye-shirya na sauya sheka daga PDP zuwa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.

Gwamna Kefas dai na daya daga cikin gwamnonin PDP da ba su halarci babban taron jam'iyyar na kasa da ke gudana a Ibadan, babban birnin jihar Oyo ba.

Kara karanta wannan

Ana cikin taron PDP na kasa a Ibadan, tsohon gwamna Abia ya fice daga jam'iyyar

Gwamna Agbu Kefas.
Hoton Gwamna Agbu Kefas yana jawabi a fadar gwamnatin Taraba Hoto: Agbu Kefas
Source: Facebook

Yaushe gwamnan Taraba zai koma APC?

Tashar Channels tv ta ce yayin da ake maganar rashin halartarsa, gwamnan Taraba ya bayyana cewa zai fita daga PDP tare da shiga APC a hukumance ranar Laraba, 19 ga Nuwamba, 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan ya sanar da hakan ne yayin duba aikin gyaran filin wasa na Jolly Nyame Stadium, iwurin da ake shirin gudanar da bikin sauya shekar tasa a makon gobe.

A cewar Agbu Kefas, wannan mataki da ya dauka na komawa APC ba don wani buri na kansa ba ne, sai don makomar al’ummar Taraba.

Gwamna Kefas ya ce:

“A ranar 19 ga Nuwamba, 2025 zan sauya sheƙa daga PDP zuwa APC a hukumance. Wannan tafiya ba ta mutum guda ba ce, ta shafi kaddarar al’ummar Jihar Taraba. Mun shirya tarbar manyan baƙi da dama.”

APC ta kafa wa Gwamna Kefas sharadi?

Da aka tambaye shi ko jam’iyyar APC ta gindaya masa sharadi kafin karɓarsa, Gwamna Kefas ya ce jawabin da zai yi a wajen taron zai fayyace komai, ya bar jama’a su yi hukunci da kansu.

Kara karanta wannan

An nemi gwamnonin jam'iyyar PDP 3 an rasa a babban taron da ake yi a Ibadan

A nata bangaren, majalisar zartarwar jihar Taraba ta nuna cikakken goyon bayanta ga gwamnan, ta bakin Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Muslim Aruwa.

A ruwayar Vanguard, kwamishinan ya ce:

“Gwamna shugabannin mu ne. Inda ya nufa, nan muke, ko APC, ko SDP, ko ADC. Wannan mataki na hada inuwa daya da gwamnatin tarayya zai taimaka wajen samar da karin ci gaban jihar, ba don wata bukata ta kashin kai ba.”
Gwamna Kefas.
Hoton Gwamna Agbu Kefas da tutar jam'iyyar APC Hoto: Agbu Kefas
Source: Facebook

Muslim Aruwa ya ƙara da cewa wannan tafiya ba ta gwamna kaɗai ba ce, “ta daukacin al’ummar Jihar Taraba ne, kuma muna tare da shi dari biA dari.”

Tsohon gwamnan Abia ya bar PDP

A baya, kun ji labarin cewa tsohon Gwamnan Jihar Abia kuma tsohon Sanata mai wakiltar Abia ta Tsakiya, Sanata Theodore Orji, ya fice daga jam’iyyar PDP.

Sanata Orji wanda ya mulki jihar Abia na tsawon shekaru takwas, ya ce ya yanke shawarar fita daga PDP ne bayan tattaunawa iyalai da abokansa na siyasa.

Hakan na kunshe ne a cikin wata wasika da ya aikawa shugaban PDP na Umuahia Ward 1, wacce ta shiga hannun manema labarai ranar Asabar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262