Shugaban NIWA Ya Yi Murabus daga Mukamin da Tinubu Ya Nada Shi, Zai Nemi Takarar Gwamna

Shugaban NIWA Ya Yi Murabus daga Mukamin da Tinubu Ya Nada Shi, Zai Nemi Takarar Gwamna

  • Asiwaju Bola Oyebamiji ya yi murabus daga mukamin shugaban hukumar kula da harkokin ruwa ta Najeriya (NIWA)
  • Tun a watan Oktoba, 2023, shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada Oyebamiji a wannan mukami, ya yi shekaru biyu yana jagoranci
  • Oyabamiji ya gode wa Shugaba Tinubu da Ministan Harkokin Teku da Tattalin Arzikin Ruwa, Gboyega Oyetola bisa damar da suka ba shi

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Shugaban Hukumar Kula da Ruwan Cikin Gida ta Kasa (NIWA), Asiwaju Bola Oyebamiji (AMBO), ya yi murabus daga kan mukaminsa.

Shugaban NIWA ya ajiye mukaminsa a gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ne domin mayar da hankali kan burinsa na tsayawa takarar gwamnan Jihar Osun a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Tsohon shugaban NIWA, Oyebamiji.
Hoton shugaban hukumar NIWA ta kasa, Asiwaju Bola Oyebamiji, wanda ya yi murabus Hoto: @RealFikayomi
Source: Twitter

The Nation ta tattaro cewa Shugaba Tinubu ne ya nada Oyebamiji a matsayin shugaban NIWA a ranar 25 ga watan Oktoba, 2023.

Kara karanta wannan

Ana batun matashin soja da Wike, Tinubu ya yi magana kan jarumtar sojojin Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban hukumar NIWA ya yi murabus

Sai dai a yanzu Oyebamiji, wanda ya kafa tafiyar siyasa a inuwar APC mai suna AMBO, ya ajiye wannan mukami da Tinubu ya ba shi saboda zai fito takarar gwamna a Osun.

Bayanai sun nuna cewa za a gudanar da zaben fidda gwani na APC a ranar 13 ga Disamba, 2025.

Mai magana da yawun tafiyar AMBO, Adebayo Adedeji, ya tabbatar da murabus ɗin Oyebamiji a cikin wata sanarwa da ya rabawa menama labarai ranar Juma'a.

A sanarwar, tsohon shugaban NIWA ya gode wa Shugaba Tinubu da Ministan Harkokin Teku da Tattalin Arzikin Ruwa, Gboyega Oyetola, bisa damar da suka ba shi ya yi wa kasa hidima.

Ci gaba da Oyebamiji ya samar a NIWA

A rahoton Leadership, Adedeji ya ce:

“A cikin shekaru biyu da ya jagoranci NIWA, Oyebamiji ya kafa shugabancina gari, inda ya yi amfani da kwarewarsa ta kusan shekaru 40 a harkokin gwamnati da na ƙasa-ƙasa wajen kawo sabbin tsare-tsare da inganta ayyukan hukumar.”

Kara karanta wannan

"Za a iya kifar da shi": Amaechi ya hango hanyar kifar da Tinubu a zaben 2027

“A karkashin jagorancinsa, an rage mace-mace da hadurra a kan hanyoyin ruwa na cikin gida da fiye da kashi 70 cikin 100.
"Ya kuma daga kimar wayar da kan jama’a game da tsaron ruwa zuwa wani mataki da ba a taɓa gani ba, tare da inganta walwalar ma’aikata.”

Adedeji ya ce yayin da Oyebamiji ke shirin shiga sabon babi tafiyar siyasar sa, yana da niyyar kawo nagartaccen shugabanci da aikin yi ga al’ummar Jihar Osun.

Shugaba Tinubu da Oyebamiji.
Hoton Shugaba Bola Ahmed Tinubu da tsohon shugaban NIWA, Asiwaju Oyebamiji
Source: Twitter

Tinubu ya sabunta nadin Buba Marwa

A wani rahoton, kun ji cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake naɗa Birgediya-Janar Mohammed Buba Marwa (Mai ritaya) a matsayin shugaban hukumar NDLEA ta kasa.

Wannan na zuwa ne bayan kammala wa’adinsa na farko da ya fara bayan tsohon shugaban ka,Marigayi Muhammadu Buhari ya nada shi a watan Janairu 2021, yanzu zai wuce wa'adi na biyu.

Kara karanta wannan

Tinubu ya aika sakon taya murna ga tsohon gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau

Tun bayan zuwansa NDLEA, ya jagoranci manyan samame da kama mutane sama da 73,000 da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, tare da kwace ƙwayoyi daban-daban.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262