Kasa da Awanni 24, Kotu Ta Dakatar da Babban Taron PDP na Kasa Saboda Sule Lamido

Kasa da Awanni 24, Kotu Ta Dakatar da Babban Taron PDP na Kasa Saboda Sule Lamido

  • Yayin da shirye-shiryen taron PDP suka yi nisa, babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta gamsu da hujjojin Sule Lamido
  • Mai shari'a Peter Lifu ya umarci INEC ta tsame hannunta daga taron PDP har sai an sanya tsohon gwamnan Jigawa a cikin 'yan takara
  • Sule Lamido ya kai kara gaban kotun ne kan hana shi shiga takarar kujerar shugaban PDP na kasa, ya ce hakan ya saba wa doka

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigera - Babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta dakatar da babban taron jam'iyyar PDP na kasa, wanda aka shirya farawa daga gobe Asabar, 15 ga watan Nuwamba, 2025.

Babbar jam'iyyar adawa ta Najeriya watau PDP ta tsara gudanar da babban taron a ranakun Asabar da Lahadi, 15 da 16 ga Nuwamba, 2025 a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Kara karanta wannan

Manyan PDP 2 sun ja daga a kan babban taron jam'iyya na kasa

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido.
Hoton tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido Hoto: Sule Lamido
Source: Facebook

Kotu ta dakatar da babban taron PDP

Jaridar Vanguard ta tattaro cewa a hukuncin da mai shari’a Peter Lifu ya yanke yau Juma'a, 14 ga watan Nuwamba, kotun ta kuma dakatar da taron kasa da awanni 24 kafin farawa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotun ta dauki wannan mataki ne a karar da tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya shigar, yana jalubalantar matakin PDP na hana shi takarar shugaban jam'iyya.

Kotun ta kuma hana Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) sa ido, sa hannu ko kuma amincewa da sakamakon kowanne taron da PDP za ta gudanar ba tare da an haɗa da Sule Lamido, a matsayin ɗan takara ba.

Sule Lamido ya yi nasara kan PDP

Kotun ta ce shaidun da ke gabanta sun nuna cewa an hana tsohon gwamna, Sule Lamido damar karɓar fam ɗin neman takarar kujerar Shugaban Jam’iyyar na ƙasa ba bisa ka’ida ba.

Kara karanta wannan

PDP ta yi watsi da Wike da mutanensa, ta ce 'babu fashi' kan taronta na Oyo

A cewar mai shari'a Peter Lifu, matakin hana tsohon gwamnan damar sayen fom domin tsayawa takara ya saba wa Kundin Tsarin Mulki da Dokokin Jam’iyyar PDP.

Kotu ta bayyana cewa a doka, nauyi ne a kan jam’iyyar PDP ta tabbatar da cewa ’ya’yanta suna samun damar yin aiki ta hanyar samar da yanayi da zai ba su damar cimma burinsu na siyasa.

Jagororin PDP na kasa.
Hoton shugaban PDP na kasa, Umar Damagum da wasu masu ruwa da tsaki a hedkwatar jam'iyyar da ke Abuja Hoto: @officialPDPNig
Source: Twitter

Domin kwato masa hakkinsa, alkalin babbar kotun tarayya ya ce dole a dakatar da duk wani shirin babban taron PDP har sai wanda ke kara ya karbi fam kamar yadda doka ta tanada.

Bugu da kari, ya umarci PDP ta dakatar da taron har sai Sule Lamido ya sayi fam, ya yi yakin neman zabe kuma ya taragoya baya, cewar rahoton The Nation.

PDP ta kafe kan gudanar da taro a Oyo

A wani labarin, kun ji cewa jam'iyyar PDP ta yi fatali da masu kawo mata tangarda, ta jaddada cewa ba gudu ba ja da baya wajen gudanar taronta na kasa a Ibadan.

Shugaban kwamitin shirya taron jam’iyyar PDP, Gwamna Umaru Fintiri, ya tabbatar da cewa jam’iyyar za ta gudanar da gagarumin taronta a birnin Ibadan kamar yadda aka tsara.

Kara karanta wannan

Rikicin PDP: Saraki ya samo mafita ga babbar jam'iyyar adawa

Wannan dai na zuwa ne bayan tsagin ministan Abuja, Nyesom Wike sun dage wajen ganin taron bai yiwu kamar yadda aka tsara ba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262