Bayan Gwamnoni 2 Sun Fita, Gwamnan PDP Ya Kawo Karshen Jita Jitar Zai Koma APC

Bayan Gwamnoni 2 Sun Fita, Gwamnan PDP Ya Kawo Karshen Jita Jitar Zai Koma APC

  • Ana rade-radin cewa Gwamna Ademola Adeleke zai bi sahun gwamnonin jihohin Enugu da Baylesa wajen ficewa daga PDP
  • Gwamma Adeleke ya musanta duka rahotanni da ake jingina masa cewa yana shirin barin PDP tare da komawa APC mai mulkin kasa
  • Ya ce rikicin da ke faruwa a PDP zai zama tarihi domin sun fara tattaunawa domin warware duk wani sabani a tsakanin 'ya'yan jam'iyyar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Osun - Gwamna Ademola Adeleke na Jihar Osun ya ce babu wani shirin da yake yi na komawa jam’iyyar APC mai mulkin kasar nan.

Gwamnan yana nan daram a jam'iyyar PDP, inda ya jaddada cewa suna ci gaba da zaman tattaunawa domin zakulo duk wasu matsaloli tare da magance su.

Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun.
Hoton Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun a wurin taro Hoto: @AAdeleke01
Source: Twitter

Ademola Adeleke ya fadi haka ne yayin hira da yan jarida bayan taron farko da kwamitin shirya gangamin PDP ya gudanar a Abuja, cewar Daily Trust.

Kara karanta wannan

A kai kasuwa: APC ta yi watsi da 'yunkurin sauya shekar' gwamnan Filato

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

PDP na kokarin shawo kan rikicinta

Gwamnan Osun ya bayyana rikicin da ake gani a jam’iyyar PDP a matsayin lamarin cikin gida na ’yan uwa da za a warware shi nan ba da jimawa ba.

A cewarsa:

“Muna ci gaba da tarurruka, muna tattauna matsalolinmu na cikin gida. Wannan lamari ne na iyali, ba ma so wani daga waje ya ƙara masa suga, barkono ko gishiri. PDP gida ɗaya ce, kuma mun san yadda za mu tafiyar da al’amuranmu.
“Mun kammala taron farko na kwamitin tsara masaukin baki. Kowa ya halarta, kuma mun warware duk matsalolin da suka taso domin babban taron mu ya gudana lafiya.”

Gwamna Adeleke ya tabo masu sauya sheka

Wannan kalamai na Adeleke na zuwa ne a daidai lokacin da Gwamnan Enugu, Peter Mbah ya sauya sheka daga PDP zuwa APC, yayin da Gwamna Douye Diri na Bayelsa ya fita daga jam'iyyar.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya fadi hanya 1 da APC za ta iya lashe zaben gwamna a jihar Oyo

Da yake tsokaci kan masu sauya sheƙa, Gwamna Adeleke ya ce ba su damu ba domin kowane ɗan siyasa yana da ’yancin yanke shawarar da yake so, amma hakan ba zai shafi karfin jam’iyyar PDP ba.

"Har yanzu PDP tana da mambobi masu ƙarfi da goyon baya a faɗin Najeriya. Don haka damu da masu fita daga cikinta ba,” in ji shi.
Gwamna Ademola Adeleke.
Hoton Gwamna Ademola Adeleke a gidan gwamnatin Osun Hoto: @AAdeleke01
Source: Instagram

Gwamnan Osun na shirin komawa APC?

Ya kuma musanta jita-jitar da ke cewa yana shirin komawa APC saboda yana da abokai a cikin jam’iyyar.

A rahoton Daily Post, Adeleke ya kara da cewa:

“Ni mutum ne mai wayewa. Idan abokaina da ke cikin APC suka gayyace ni zuwa bikin aure ko wani taron zamantakewa, zan halarta. Amma hakan ba yana nufin na koma APC ba.
"Yanzu haka, ni ne Mataimakin Shugaban Kwamitin Shirya Babban Taron PDP da za a gudanar a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, kuma har yanzu ina da alaka mai kyau da PDP.”

Gwamna Adeleke zai koma jam'iyyar ADC?

A wani labarin, kun ji cewa gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya musanta jita-jitar cewa zai sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa ADC.

Kara karanta wannan

ADC ta yi babban kamu, tsohon shugaban PDP ya yi murabus bayan shekaru 22

Gwamna Adeleke ya nesanta kansa daga batun komawa ADC, inda ya tabbatar da cewa har yanzu yana nan daram a jam’iyyar PDP.

Mai magana da yawun gwamnan Osun, Olawale Rasheed ya bayyana cewa rahoton sauya shekar karya ce da wasu ke yadawa domin tayar da rudani a zukatan jama’a.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262