'Mu fa sai Jonathan,' : Kungiyar Arewa Ta Dage Tsohon Shugaban Kasa Ya Sake Takara

'Mu fa sai Jonathan,' : Kungiyar Arewa Ta Dage Tsohon Shugaban Kasa Ya Sake Takara

  • Wata ƙungiyar a Arewacin Najeriya ta bayyana wanda take goyon baya a zaben shekarar 2027 da ke tafe
  • Kungiyar da ke marawa PDP baya ta ce babu ja da baya kan marawa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan baya a zaben 2027
  • Ta yaba da jagorancin Umar Damagum, tana mai cewa lokaci ya yi da ‘yan jam’iyyar za su haɗa kai domin dawo da mulki hannun PDP

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kebbi - Tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan na ci gaba da samun goyon bayan kan takara a 2027.

Ƙungiyar da ke goyon bayan Jam’iyyar PDP a Arewa ta bayyana cewa babu ja da baya kan marawa tsohon shugaban ƙasa baya.

Kungiya ta bayyana Jonathan a matsayin mafi dacewa a zaben 2027
Tsohon shugaban kasa a Najeriya, Goodluck Jonathan. Hoto: Goodluck Jonathan.
Source: Twitter

Jonathan ya samu kwarin guiwar takarar 2027

Rahoton Vanguard ya ce kungiyar ta ce za ta goyi bayansa ne domin tsayawa takarar shugaban ƙasa a shekarar 2027.

Kara karanta wannan

Atiku ya shiga sahun masu neman fito da shugaban kungiyar ta'addanci da aka kama tun 2021

Wannan sanarwar ta fito ne bayan taronsu na takwas da aka gudanar a Birnin Kebbi daga ranar 8 zuwa 9 ga watan Oktoba, 2025.

Kungiyar ta ce babu shakka Goodluck Jonathan ne mutum mafi dacewa da zai gyara sunan jam’iyyar, tana mai cewa batun cancanta ya riga ya samu.

Sun bayyana Jonathan a matsayin mutum mai son zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba, wanda ya sadaukar da kansa don zaman lafiyar ƙasa lokacin da ya mika mulki cikin lumana a 2015.

Shugaban PDP ya samu goyon bayan 'yan jam'iyya

Ƙungiyar ta bayyana goyon bayanta ga mukaddashin shugaban jam’iyyar, Ambasada Iliya Umar Damagum.

Ta ce Damagum yana jagorantar sake gina jam’iyyar ta hanyar karfafa haɗin kai da ladabi tsakanin mambobinta a faɗin ƙasar nan.

A cewar ƙungiyar, lokaci ya yi da ‘yan jam’iyyar za su haɗa kai domin tabbatar da dawowar PDP kan mulki a 2027.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar ADC ta kafa sharuda 4 kafin ba 'yan siyasa tikitin takara a 2027

Jonathan ya sake samun goyon baya kan takara a 2027
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan. Hoto: Goodluck Jonathan.
Source: Twitter

Korafi kan wasu shugabannin PDP a Najeriya

Sai dai ƙungiyar ta nuna damuwa kan wasu shugabannin jam’iyyar da ke cin moriyar gwamnati mai ci, tana zargin wasu daga cikin NWC suna aiki da APC.

Ta ce irin wannan ba zai taimaka ba wajen farfaɗo da jam’iyyar, saboda haka dole ne a ɗauki mataki mai tsauri, cewar rahoton Punch.

Haka kuma, ƙungiyar ta zargi ministan Abuja Nyesom Wike da haddasa rarrabuwar kawuna a jam’iyyar PDP, tana cewa ya zama dole a dakatar da tasirinsa kafin ya lalata jam’iyyar.

A ƙarshe, ƙungiyar ta jaddada amincinta ga shugabancin PDP tare da alƙawarin ci gaba da aiki tukuru don kafa ingantacciyar jam’iyya mai haɗin kai wacce za ta karɓi mulki a 2027.

An shawarci Jonathan kan takara a 2027

Kun ji cewa tsohon dan takarar gwamnan jihar Lagos, Abdul-Azeez Adeniran, ya ja kunnen tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan.

Kara karanta wannan

Dattawan Arewa sun bayyana matsayarsu kan zaben 2027, ta fadi kalan dan takararta

Kusa a APC ya bukaci Jonathan da ka da ya yi kuskuren yin takara da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027.

Adeniran ya bayyana cewa babu wani dan siyasa da zai iya kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.