Kano: Minista Ya Faɗi Wanda Suke Son ba Takara a APC domin Ƙwace Kujerar Abba

Kano: Minista Ya Faɗi Wanda Suke Son ba Takara a APC domin Ƙwace Kujerar Abba

  • Minista a gwamnatin Bola Tinubu daga jihar Kano, Yusuf Abdullahi Ata ya ce APC na da shirin lashe zaben gwamnan Kano a 2027
  • Ata ya ce babu sabani tsakanin Sanata Barau Jibrin da Murtala Sule Garo, kuma Nasiru Gawuna na iya takarar Sanatan Kano ta Tsakiya
  • APC ta fuskanci kalubale daga NNPP tun bayan nasarar Abba Kabir Yusuf a 2023, yayin da 'yan jam’iyyar ke komawa NNPP

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Karamin ministan mai kula da gidaje da raya birane, Hon. Yusuf Abdullahi Atta, ya yi magana kan zaben a Kano.

Ata ya bayyana shirin APC na kwace kujerar gwamna a Kano bayan rashin nasara a zaben 2023 da ta gabata a jihar.

Ministan Tinubu ya magantu kan kwace mulkin Kano
Minista ya ce sun shirya kwace mulki a hannun Abba Kabir a Kano. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

A wata hira da aka yi da shi a Freedom Radio Kano da Legit.ng ta bibiya, Ata ya bayyana cewa Barau zai tsaya takarar gwamnan jihar Kano.

Kara karanta wannan

Tinubu ya amince da kashe sama da N712bn a yi wa filin jirgin Legas kwaskwarima

Tasirin jihar Kano a siyasar Arewacin Najeriya

Jihar Kano ta kasance fagen daga tsakanin yan siyasa a fadin kasar duba da tasirin da take da shi a Arewacin Najeriya baki daya a bangaren siyasa.

Jam'iyyar NNPP ce ke mulki bayan kwace ragamar jagoranci daga APC mai mulkin Najeriya a zabukan 2023 da suka gabata.

An tabbatar Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben kan abokin takararsa wanda shi ne tsohon mataimakin gwamnan jihar, Dakta Nasiru Gawuna.

Minista ya sha alwashin APC za ta kwace mulki a Kano
Ministan Tinubu ya fadi shirin APC na karbe mulki a Kano. Hoto: Yusuf Abdullahi Ata, Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Ata ya fadi wanda zai tsaya takarar gwamna

Ata ya ce APC na sa ran Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, zai tsaya takarar gwamna a zaben 2027.

Sanata Barau wanda ya dade a siyasa yanzu ana kallonsa a matsayin wanda zai iya hade APC don kalubalantar NNPP.

Ya kuma karyata jita-jitar da ke cewa akwai sabani tsakanin Barau da tsohon kwamishinan kananan hukumomi, Hon. Murtala Sule Garo.

Kara karanta wannan

2027: Dino Melaye da wasu na hannun daman Atiku 2 da suka fice daga PDP zuwa ADC

Kano: Alwashin da Ata ya ci na karbar mulki

Atta ya jaddada cewa APC a Kano ta hada kai, kuma sun mayar da hankali kan dawo da mulki a jihar a 2027.

Ya ce:

"Babu rikici tsakanin Barau da Garo. Muna fatan Garo zai tsaya takarar Sanata na Kano ta Arewa."

Ya kuma ce dan takarar gwamna na APC a 2023, Nasiru Gawuna, na iya tsayawa takarar Sanatan Kano ta Tsakiya.

Ata ya ce duk dan jam’iyya na da ’yancin tsayawa takara, amma su na goyon bayan Sanata Barau don ya jagoranci Kano.

Ata ya fadi dalilin Tinubu na naɗa shi minista

Mun ba ku labarin cewa karamin ministan gidaje da ci gaban birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya ce burinsa shi ne dawo da Kano ga jam'iyyar APC a 2027.

Yayin ziyararsa ta farko a Kano bayan rantsar da shi, Yusuf Ata ya bayyana cewa nadinsa na da muhimmanci wajen karfafa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.

Ya gode wa Shugaba Bola Tinubu, inda ya jaddada kudurinsa na ciyar da APC gaba a Kano ta hanyar ziyartar jihar duk da tarin aikinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.