Sabon Shugaban APC Ya Kada Hantar 'Yan Adawa, Ya Sha Alwashi kan Zaben 2027

Sabon Shugaban APC Ya Kada Hantar 'Yan Adawa, Ya Sha Alwashi kan Zaben 2027

  • Sabon shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda ya fara dauko batun zaben shekarar 2027
  • Nentawe Yilwatda ya sha alwashin tabbatar da nasarar Bola Tinubu da sauran 'yan takarar da APC za ta tsaida lokacin
  • Shugaban na APC ya nuna cewa gwamnatin Bola Tinubu ta bullo da shirye-shirye masu yawa don tallafawa matasa

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Sabon shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya sha alwashi kan zaben shekarar 2027.

Farfesa Nentawe Yilwatda ya sha alwashin yin aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, 'yan takarar gwamna, na majalisar tarayya da na majalisun jihohi a zaɓen 2027.

Nentawe Yilwatda ya sha alwashi kan zaben 2027
Nentawe ya ce zai yi aiki don tabbatar da nasarar Tinubu a 2027 Hoto: @OfficialAPCNg
Source: Twitter

Yilwatda ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin da yake jawabi ga daruruwan magoya bayan jam’iyyar karkashin kungiyar 'APC League of Professionals', cewar rahoton jaridar Leadership.

Kara karanta wannan

ADC ta samu ƙaruwa, babban jigon PDP a Kaduna ya sauya sheƙa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Yan kungiyar dai sun kai masa ziyarar nuna goyon baya ne a sakatariyar jam’iyyar APC ta ƙasa da ke Abuja.

Me Yilwatda Nentawe ya ce kan APC?

Ya yi watsi da ikirarin da jam’iyyar ADC da sauran jam’iyyun adawa ke yi, yana mai cewa nasarorin da aka samu karkashin shirin “Renewed Hope” na gwamnatin Tinubu sun karade ko ina a faɗin ƙasar nan.

"Yaron talaka a Najeriya yanzu yana iya zuwa makaranta har matakin gaba ba tare da karɓar bashi daga ko ina ba. Gwamnati ta tanadi wannan dama."
"Wannan shi ne karo na farko da hakan ya faru a tarihin Najeriya. Gwamnati ta ajiye Naira biliyan 1.5 a bankin noma (BOA) domin tallafa wa matasa masu sha’awar shiga harkar noma."
"Ba a taɓa samun irin wannan dama ba a baya. Akwai kuɗin matasa da ake bayarwa don tallafa musu. Babu wata gwamnati da ta taɓa yin hakan. Kuma zan iya gaya muku cewa wannan dama ga matasa tana a karkashin jagorancin shugabanmu."

Kara karanta wannan

'Za mu shiga Aso Rock': Atiku ya fadi babban shirin ADC na karbar mulki a 2027

"Abin da zan fara nuna muku shi ne godiya bisa goyon bayanku, godiya bisa tsayuwar ku tare da jam’iyyarmu, godiya saboda kun yi amanna da wannan jam’iyya.”

- Farfesa Nentawe Yilwatda

Nentawe Yilwatda ya ce APC ta fifita matasa
Nentawe na son ganin Tinubu ya samu nasara a 2027 Hoto: Prof. Yilwatda Nentawe
Source: Twitter

Jam'iyyar APC na son ci gaban matasa

Shugaban jam’iyyar na kasa ya jaddada cewa manufar APC ta fi karkata ga matasa.

"Shirin Renewed Hope an yi shi ne don mutane irin ku. Kuma ina fatan yin aiki tare da ku domin tabbatar da cewa zaɓen 2027 zai samar da nasara ga shugaban kasa, ga gwamnoni, ga Sanatoci, ga 'yan majalisar tarayya da ta Jihohi."

- Farfesa Nentawe Yilwatda

Mambobin APC sun yi zanga-zanga

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu mambobin jam'iyyar APC a jihar Legas sun gudanar da zanga-zanga a gaban majalisar dokoki.

Mambobin na APC sun gudanar da zanga-zangar ne don neman shugaban jam'iyyar na jihar ya sauka daga kan mukaminsa.

Masu zanga-zangar sun zargin Cornelius Adejobi da yin karfa-karfa kan mutanen da za a ba mukamai a gwamnatocin kananan hukumomin jihar.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng