Yadda Hadakar Atiku, El Rufai Za Ta Iya Kawar da Tinubu a 2027', Umar Ardo

Yadda Hadakar Atiku, El Rufai Za Ta Iya Kawar da Tinubu a 2027', Umar Ardo

  • Tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Adamawa a ƙarƙashin inuwar SDP a zaɓen 2023, Umar Ardo, ya yi magana kan shirin kifar da Bola Tinubu
  • Umar Ardo wanda ya taba sha'awar takarar shugaban kasa ya ce haɗakar adawa za ta iya kawar da Tinubu a 2027 idan aka bi hanyar da ta dace
  • Ya bayyana cewa kafa sabuwar jam'iyya ita ce mafita idan har ƴan haɗakar suna son samun nasara a babban zaɓen 2027 da ake tunkara

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Adamawa a ƙarƙashin jam’iyyar SDP a zaɓen 2023, Umar Ardo, ya yi magana kan haɗaka don kawar da Shugaba Bola Tinubu a 2027.

Dr. Umar Ardo ya bayyana cewa akwai yiwuwar kifar da Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027 muddin ƴan adawa suka kafa sabuwar jam’iyyar siyasa.

Kara karanta wannan

"Ya gaza": Tsohon gwamna ya caccaki Tinubu kan kuntatawa 'yan Najeriya

An shawarci Atiku, El-Rufai kan hadaka
Umar Ardo ya ce 'yan hadaka za su iya kifar da Tinubu a 2027 Hoto: @atiku, @elrufai, @DOlusegun
Source: Facebook

Tsohon ɗan takarar gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake magana a shirin Morning Show na gidan talabijin na Arise Tv a ranar Laraba, 4 ga watan Yunin 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wace shawara aka ba ƴan haɗaka?

Umar Ardo wanda ƙwararren mai tsara dabarun siyasa ne kuma mai jigo a tafiyar ƙungiyar League of Northern Democrats (LND), ya nuna ƙwarin gwiwa dangane ɗunƙulewar ƴan adawa a inuwa ɗaya.

Sai dai ya amince cewa haɗakar da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ke jagoranta na fama da rashin daidaituwar ra’ayi.

Ya yi watsi da ra’ayin haɗaka ta shiga wata jam'iyya, yana mai jaddada cewa kafa sabuwar jam’iyya ce za ta bayar da wata tabbatacciyar dama ta karɓar mulki.

"Idan gaba ɗaya ƴan adawa suka haɗu suka amince da kafa sabuwar jam’iyya, akwai babban fata na samun nasara a kan Shugaba Tinubu a 2027."

Kara karanta wannan

Tinubu ya ƙara ƙarfi, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ya haƙura da neman mulki a 2027

“An kafa kwamitoci biyu a cikin haɗaka, ɗaya don duba yiwuwar haɗewa da wata jam’iyya da ake da ita a yanzu, ɗaya kuma don nazarin yiwuwar rajistar sabuwar jam'iyya."
"Dukkanin kwamitocin sun kammala aikinsu, kuma daga abin da na gani, hujjar haɗuwa da wata jam’iyya ba ta da ƙarfi.

- Umar Ardo

Ana yunkurin kifar da Bola Tinubu a 2027
An bukaci 'yan hadaka su kafa sabuwar jam'iyya don kifar da Tinubu Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Umar Ardo ya nuna ƙwarin gwiwa kan haɗaka

Umar Ardo ya jaddada cewa nasarar haɗakar za ta dogara ne bisa amfani da dabarar da ta dace.

"Idan aka ɗauki hanyar da ta dace da kuma shawarwari nagari, ina da yaƙinin cewa samun nasara abu ne wanda zai yiwu."

- Umar Ardo

Ƙungiyar LND ta kafa sharaɗin shiga haɗaka

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar LND wacce Malam Ibrahim Shekarau ke jagoranta ta yi magana kan shiga haɗakar jam'iyyun ƴan adawa.

Ƙungiyar LND ta buƙaci su Atiku Abubakar da sauran ƴan haɗaka su kafa sabuwar jam'iyya don tunkarar zaɓen 2027.

LND ta bayyana cewa kafa sabuwar jam'iyya ce kawai abin da zai sanya ta shiga haɗakar ta ƴan adawa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng