"Ina Goyon Bayan Tinubu": Kan Gwamnoni Ya Fara Rabuwa saboda Dokar Ta Ɓaci a Ribas

"Ina Goyon Bayan Tinubu": Kan Gwamnoni Ya Fara Rabuwa saboda Dokar Ta Ɓaci a Ribas

  • Gwamnan Edo, Monday Okpebholo ya tsame kansa daga matsayar gwamnonin Kudu maso Kudu kan dokar ta ɓaci a jihar Ribas
  • Okpebholo ya bayyana cewa ya na da yaƙinin cewa matakin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya ɗauka shi ne ya fi dacewa
  • Tun farko gwamnonin Kudu maso Kusu sun yi watsi da ayyana dokar ta ɓaci a Ribas, sun ce hakan illa ce babba ga demokuraɗiyya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Edo - A wani mataki mai cike da rudani, gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya yi magana kan matsayar wasu gwamnonin yankin Kudu Maso Kudu kan dokar ta ɓaci a Ribas.

Tun farko dai gwamnonin shiyyar Kudu maso Kudancin Najeriya sun yi fatali da dokar ta ɓacin da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana a jihar Ribas.

Kara karanta wannan

'Suna da Sarkinsu, mu na da namu': An fadi lokacin da Aminu Ado zai yi sallar idi a Kano

Gwamna Okpebholo.
Gwamnan Edo ya goyi bayan Tinubu, ya nesanta kansa daga matsayar gwamnonin Kudu maso Kudu Hoto: Monday Okpebholo
Asali: Twitter

Gwamna Okpebholo na jihar Edo ya nesanta kansa da wannan matsaya ta gwamnonin, kamar yadda Leadership ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan na kunshe a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Edo, Fred Itua ya fitar ranar Alhamis, 20 ga watan Maris, 2025.

Gwamnan Edo ya goyi bayan Bola Tinubu

Gwamna Okpebholo ya ce ba a tuntube shi ba ko neman shawararsa kafin takwarorinsa su bayyana matsayinsu kan batun dokar ta-baci a jihar Ribas.

Sanarwar ta bayyana cewa gwamnan ya aminta da ‘yancin sauran gwamnonin yankin su fadi ra’ayinsu, amma shi bai amince da wata matsaya da ke adawa da matakin da shugaba Tinubu ya ɗauka ba.

“Shugaban ƙasa kuma kwamandan askarawan Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya fahimci abubuwan da ke faruwa a jihar Ribas kuma ya ɗauki matakan da suka dace domin dakile rikicin da ke ci gaba da ta’azzara.
“Gwamna Okpebholo ya na goyon bayan duk matakan da shugaba Tinubu ya ɗauka domin kawo zaman lafiya da dawwamar da kwanciyar hankali a jihar Ribas da yankin Kudu maso Kudu baki ɗaya."

Kara karanta wannan

Aiki zai dawo sabo: Gwamnoni 12 za su maka Tinubu a kotu kan Fubara

- in ji Fred Itua.

Kawunan gwamnonin Kudu ya rabu

Tun bayan ayyana dokar ta-baci a jihar Ribas, gwamnonin yankin Kudu maso Kudu suka nuna adawarsu da matakin, suna mai cewa cin zarafin dimokuradiyya ne.

Sai dai Gwamna Okpebholo ya bayyana cewa matakin da shugaban ƙasa ya ɗauka na da tushe, kuma zai taimaka wajen dakile rikicin siyasa da ke ƙara ƙamari a jihar.

Wannan mataki da Gwamnan Edo ya ɗauka wata ɓaraka ce a ƙungiyar gwamnonin Kudu maso Kudu, wacce Ribas take mamba a ciki, The Nation ta kawo.

Ana ganin hakan ba zai nasaba da siyasa ba kasancewar Gwamna Okpebholo ɗan jam'iyyar APC ne saɓanin sauran gwamnonin jihohin Kudu maso Kudu.

Har yanzu dai ana ci gaba da samun martani daga masu ruwa da tsaki kan batun Ribas, inda wasu ke goyon bayan matakin dokar ta-baci, yayin da wasu ke nuna adawarsu.

Fubara ya musanta zarge-zargen Tinubu

Kara karanta wannan

Fubara: Kwankwaso ya hade da Atiku, El Rufa'i, Obi kan rikicin Ribas

A wani labarin, kun ji cewa dakataccen gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara ya musanta laififfukan da Bola Tinubu ya ɗora masa a jawabin da ya yi.

Fubara ya jaddada cewa ya yi duk mai yiwuwa wajen kare albarkatun mai da ke jihar, kum saura ƙiris a kammala gina sabuwar Majalisar Dokoki.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng