'Yadda El Rufai Ke Yi Wa Siyasarsa Illa bayan Rikito Rigima da APC, Ribadu da Uba Sani'

'Yadda El Rufai Ke Yi Wa Siyasarsa Illa bayan Rikito Rigima da APC, Ribadu da Uba Sani'

  • An bayyana rigimar da Nasir El-Rufai ke yi da Gwamna Uba Sani, APC, da NSA Nuhu Ribadu ka iya lalata masa siyasa
  • Masanin siyasa, Kelly Agaba, ya ce hakan na iya shafar siyasar El-Rufai a 2027 duba da shirin haɗaka da yake yi
  • Agaba ya ce sukar El-Rufai ga jagorancin APC da matsalolinsa da Uba Sani da Ribadu na iya nisantar da shi daga manyan jiga-jigai a jam’iyyar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Tsohon gwamnan Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, yana cikin rikice-rikice da Gwamna Uba Sani, jam’iyyar APC mai mulki, da NSA Nuhu Ribadu.

Wani masanin siyasa, Kelly Agaba, ya bayyana yadda hakan zai iya shafar siyasarsa a 2027 da gaba.

An fadi illar da El-Rufai ke yi wa kansa kan zaben 2027
Masanin siyasa ya fadi yadda Nasir El-Rufai ke yi wa siyasarsa illa a gaba. Hoto: Uba Sani, Nasir El-Rufai, Nuhu Ribadu.
Asali: Facebook

An fadawa El-Rufai illar da yake yiwa siyasarsa

Kara karanta wannan

Malamin addini ya shiga siyasa a Kano, ya jagoranci magoya bayansa zuwa jam'iyyar APC

A wata hira da Legit.ng, Agaba ya ce sukar El-Rufai ga jagorancin APC da matsalolinsa da Uba Sani da Ribadu na iya nisantar da shi daga manyan jiga-jigai a jam’iyyar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Agaba ya ce fuskantar rikice-rikice da yawa lokaci guda yana da hatsari a siyasar Najeriya.

Ya ce hakan na iya rage wa El-Rufai karfi a jam'iyyar APC da ya sha mata wahala tun farko.

Yayin da yake mayar da martani kan kalaman El-Rufai game da APC, Uba Sani, da Nuhu Ribadu, masanin ya ce irin wadannan kalamai suna ta da cece-kuce.

"Maganganun El-Rufai kan APC, Gwamna Uba Sani da Nuhu Ribadu sun haddasa mahawara sosai, fuskantar rikice-rikice da yawa lokaci guda na da hadari a siyasar Najeriya."
"Tsokacin El-Rufai kan shugabancin APC da matsalolinsa da Uba Sani da Ribadu na iya nisantar da shi daga jiga-jigai a jam’iyyar, hakan na iya shafar siyasarsa a 2027."

Kara karanta wannan

"Za mu kawo karshen mulkin kama karya," PDP ta musanta baraka a cikinta

Cewar Agaba

Matsalar da El-Rufai ka iya fuskanta a siyasarsa

Da yake magana kan illar fuskantar rikice-rikice da yawa, Agaba ya ce hakan na iya dagula alakarsa da manyan ‘yan siyasa.

Masanin ya ce hakan na iya hana El-Rufai samun goyon baya a gaba wanda ka iya shafar burinsa a nan gaba.

El-Rufai: An dura kan Gwamna Uba Sani

Kun ji cewa Gwamna Uba Sani ya taya tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai murnar zagayowar haihuwarsa, inda ya yi masa fatan alheri.

Sai dai sakon taya murnar ya jawo ka-ce-na-ce a kafofin sadarwa bayan rade-radin rashin jituwa tsakaninsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.