Abinci Ya Ƙare: Gwamna Ya Tattara Duka Masu Muƙaman Siyasa, Ya Kore Su daga Aiƙi

Abinci Ya Ƙare: Gwamna Ya Tattara Duka Masu Muƙaman Siyasa, Ya Kore Su daga Aiƙi

  • Gwamna Abdullahi Sule ya sallami dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa a gwamnatinsa a jihar Nasarawa, ya na mai yi masu fatan alheri
  • Sule, wanda bai jima da korar kwamishinoni ba ya faɗi haka ne a taron bankwana da ya yi da waɗanda lamarin ya shafa a faɗar gwamnati
  • Bugu da ƙari, gwamnan ya rantsar da sabon sakataren gwamnati, Labaran Magaji, wanda shi ne tsohon kwamishinan shari'a kuma Antoni Janar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Nasarawa - Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya sanar da sallamar dukkanin masu rike da mukaman siyasa a gwamnatinsa.

Gwamna Sule ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a, 7 ga Fabrairu, 2025 a gidan gwamnatin jihar Nasarawa da ke birnin Lafiya.

Gwamna Abdullahi Sule.
Gwamna Sule ya sallami dukkan hadiman da ya naɗa a muƙaman siyasa a jihar Nasarawa. Hoto: Abdullahi A. Sule
Source: Facebook

Jaridar The Nation ta tattaro cewa Gwamna Sule ya sallami masu rike da muƙaman siyasa ne makonni ƙalilan bayan ya rushe majalisar zartarwa ta jihar.

Kara karanta wannan

Rusau: Abba zai kashe biliyoyi wajen yin asibiti, tituna, lantarki a Rimin Zakara

Gwamnan Nasarawa ya yi bankwana da hadimansa

Sule ya sanar da matakin a taron ban kwana da ya gudanar da manyan mashawarta, hadimai na musamman, da sauran masu rike da mukaman siyasa a zauren majalisar zartarwa na fadar gwamnatinsa.

A yayin jawabinsa, gwamnan ya gode masu dukka bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar a lokacin da suke rike da mukamansu.

Ya kuma bada tabbacin cewa wasu daga cikinsu na iya samun damar sake dawowa cikin gwamnati a wasu muƙaman da zai naɗa nan gaba.

Gwamna Sule ya yi sababbin nade-nade

Bayan sallamar masu riƙe da muƙaman siyasa, gwamnan ya rantsar da sabon sakataren Gwamnati, Barista Labaran Magaji, rahoton Vanguard.

Barista Labaran shi ne tsohon kwamishinan shari'a kuma Antoni-Janar na jihar wanda ya rasa muƙaminsa lokacin da gwamnan ya sallami dukkan kwamishinoni.

Baya ga haka, Abdullahi Sule ya rantsar da sabon shugaban yankin Udage da ke ƙaramar hukumar Nasarawa da shugaba da ƴan majalisar gudanarwa na kwalejin ilimi ta Akwanga.

Kara karanta wannan

Gwamnan Zamfara ya yi alhinin rasuwar Almajirai a gobara, ya fadi matakin ɗauka

Gwamna Sule. ya buƙaci waɗanda aka rantsar da su zage dantse kuma su taimakawa gwamnatinsa wajen cika manufofinta na alheri ga al'umma.

Ina aka kwana kan naɗa kwamishinoni?

Gwamna Sule, wanda a farkon watan Janairu ya rushe majalisar zartarwa ta jihar, ya ce tuni ya mika sunayen mutum 16 da ya zaba domin naɗa su a kwamishinoni ga majalisar dokokin jihar domin tantancewa.

Ana sa ran sababbin nade-nade za su kara habaka tafiyar gwamnatin Abdullahi Sule da samar da ci gaba ga al’ummar jihar Nasarawa.

APC ba ta tsoron haɗewar ƴan adawa

A wani rahoton, kun ji cewa Gwamna Abdullahi Sule ya ce jam'iyyar APC ba ta tsoron shirin da wasu manyan ƴan adawa ke yi domin haɗe wa guri ɗaya a zaɓen 2027.

Gwamna Sule.ya ce ba ya jin tsoron haɗakar ƴan adawa domin nasarar APC ta ta'allaka ne da irin ayyukan alherin da ta kawo wa ƴan Najeriya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262