Atiku Ya Manta da Rashin Jituwa a Siyasa, Ya Jajanta da Yayan Gwamna Ya Rasu

Atiku Ya Manta da Rashin Jituwa a Siyasa, Ya Jajanta da Yayan Gwamna Ya Rasu

  • Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya tura sakon ta'azziya kan rashin dan uwan Gwamna Seyi Makinde
  • Atiku ya jajanta tare da nuna takaici kan rasuwar babban yayansa mai suna Sunday Makinde a yau Juma'a
  • Tsohon dan takarar shugaban kasa a PDP ya kuma mika ta'aziyyata ga dangin marigayin tare da yin addu'ar Allah ya ba su hakurin jure wannan babban rashi
  • Hakan ya biyo bayan sanar da rasuwar marigayin wanda shi ne babban dan uwan gwamnan a yau Juma'a 24 ga watan Janairun 2025

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon dan takarar shugaban kasa a PDP, Atiku Abubakar ya tura sakon ta'azziya ga Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo.

Atiku ya jajanta wa gwamnan bayan rasuwar babban yayansa mai suna Injiniya Sunday Makinde a yau Juma'a 24 ga watan Janairun 2025.

Kara karanta wannan

Watanni da aure, diyar mataimakiyar gwamna ta yi bankwana da duniya yayin naƙuda

Atiku ya jajanta wa gwamna bayan mutuwar yayansa
Atiku Abubakar ya tura sakon ta'azziya ga gwamna Seyi Makinde bayan rasuwar yayansa. Hoto: Atiku Abubakar, Seyi Makinde.
Asali: Facebook

Yayan Gwamna Seyi Makinde ya kwanta dama

Atiku ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a yau Juma'a 24 ga watan Janairun 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan sakon ta'azziya na zuwa ne bayan Allah ya yi wa Sunday Makinde, yayan Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo rasuwa da daddare, wayewar garin yau Juma'a, 24 ga watan Janairu.

Ɗaya daga cikin ƙannensa ya bayyana cewa Injiniya Sunday Makinde ya rasu ba zato ba tsammani da misalin ƙarfe 3:20 na dare.

Tuni dai ƴan uwa da abokan arziki suka fara jimami da ta'aziyyar rashin yayan mai girma gwamna, wanda ya rasu ya bar ƴan uwa, 'ya'ya da jikoki.

Atiku ya tura sakon ta'azziya ga Seyi Makinde

A cikin sanarwar, Atiku ya ce ya shiga cikin alhini kan rasuwar tare da yi masa addu'ar samun rahama da sauran wadanda suka riga mu gidan gaskiya.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya shiga yanayi da yayan gwamna ya riga mu gidan gaskiya

Tsohon mataimakin shugaban kasa ya kuma mika ta'aziyyata ga dangin marigayin tare da addu'ar Allah ya ba su hakurin jure wannan babban rashi.

Daga bisani, ya yi addu'ar Allah ya jikansa da rahama, ya sanya shi cikin kwanciyar hankali da salama a rayuwar lahira.

Atiku ya yi addu'ar samun rahama ga marigayin

"Cikin alhini, ina mika ta’aziyyata ga Gwamnan Jihar Oyo, Injiniya Seyi Makinde, kan rasuwar babban yayansa, Sunday Makinde."
"Ina kuma mika ta’aziyyata ta musamman ga iyalan marigayin tare da yin addu’ar Allah ya ba su karfin hali da hakurin jure wannan babban rashi."
"Allah ya jikansa da rahama, ya sanya shi cikin kwanciyar hankali da salama a rayuwar lahira."

- Atiku Abubakar

Tsohon hadimin Atiku ya kwanta dama

Kun ji cewa hadimin tsohon mataimakin shugaban kasa, Hon. Shima Ayati ya rasu a Makurdi bayan gajeriyar rashin lafiya.

Ayati ya yi aiki tare da Atiku Abubakar a lokacin mulkin Olusegun Obasanjo kuma ya jagoranci kwamitin tallafin Zaki Biam a 2003.

Marigayin dan asalin karamar hukumar Ukum ta jihar Benue, ya bar siyasa domin mayar da hankali kan kasuwancinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.