Gaskiya Ta Fito da Aka Fara Zargin Minista kuma Jigon APC da Shirin Yaƙar Tinubu a 2027

Gaskiya Ta Fito da Aka Fara Zargin Minista kuma Jigon APC da Shirin Yaƙar Tinubu a 2027

  • Karamin ministan man fetur, Ekperikpo Ekpo ya musanta zargin cewa yana da hannu a wani shiri na hana Shugaba Bola Tinubu tazarce a 2027
  • Ministan ya jaddada biyayyarsa ga APC mai mulki tare da yin bayanin dalilin da ya sa aka ga alaƙa ta ƙullu tsakaninsa da gwamnan Akwa Ibom
  • Ya ce ya haɗa kai da Gwamna Umo Eno duk da ba jam'iyyarsu ɗaya ba saboda tabbatar da zaman lafiya da kawo ci gaba a jihar Akwa Ibom

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Karamin ministan albarkatun man fetur (Gas), Ekperikpo Ekpo, ya musanta zargin cewa yana da hannu a shirin yaƙar tazarcen shugaban ƙasa, Bola Tinubu a 2027.

Ministan ya karyata zargin da aka ce Gwamna Umo Eno na Akwa Ibom ya dauke shi aiki don hana Shugaba Bola Tinubu samun wa’adi na biyu.

Kara karanta wannan

"A shirye nake na tuɓe rigar kariya, na miƙa kaina ga EFCC," Gwamna ya magantu

Ekperikpo Ekpo da Bola Tinubu.
Karamin ministan albarkatun man fetur ya musanta zargin haɗa kai gwamnan Akwa Ibom domin ruguza tazarcen Bola Tinubu a 2027 Hoto:Ekperikpo Ekpo, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Ekpo ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ministan, Louis Ibah, ya fitar ranar Laraba, kamar yadda Premium Times ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ana zargin minista na shirin yakar Tinubu

Ya ce zargin ministan ya haɗa kai da Gwamna Umo Eno don kifar da Tinubu a zaɓen 2027 ya fito ne daga wata kungiya mai neman suna a jihar Akwa Ibom.

An ruwato cewa ƙungiyar mai suna, "tawagar ƴan APC masu kishi a Akwa Ibom," ta tura sakon zargin ƙaramin ministan ga shugaban ƙasa.

Ministan ya musanta zargin da ake masa

Mista Ibah ya ce:

“Za mu iya musanta wannan zargi cewa Mista Ekpo yana da hannu a wani shiri na ruguza shirin tazarcen Shugaba Tinubu."

Ya bayyana zarge-zargen a matsayin “ƙarya” da kuma “abin dariya,” yana mai jaddada cewa Mista Ekpo na nan a matsayinsa na amintaccen ɗan APC.

Kara karanta wannan

"Ba haka ya kamata ba," Peter Obi ya kawo cikas a shirin haɗakar Atiku da Kwankwaso a 2027

A cewar ministan, Gwamna Eno yana jagorantar gwamnati mai ƙaunar zaman lafiya a jihar Akwa Ibom ba tare da tsoma baki a harkokin APC ba.

Mista Ibah ya ce jajircewa da sadaukarwar ƙaramin ministan fefur ga jam'iyyar APC da manufofinta yana nan daram, babu abin da ya sauya.

Yadda Ekpo ya taimaki APC a zaɓen 2023

“Babu shakka Ekperikpo Ekpo ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa Akwa Ibom Democratic Forum (ADF), wata ƙungiyar siyasa da ta haɗa ‘yan asalin Akwa Ibom, wanda ya taimaka sosai a nasarorin da APC ta samu a zaɓen 2023.
“Ƙoƙarinsa ne ya kai ga nasarar Shugaban Majalisar Dattijai da ƴan Majalisar Wakilai 2 a zaɓen 2023, tare da shugaban ƙaramar hukumar Essien Udim da kujerun kansiloli," in ji shi.

Ƙaramin ministan albarkatun man fetur. Mista Ekpo haifaffen ƙaramar hukumar Ika ce a jihar Akwa Ibom.

Ya taba yin aiki a matsayin shugaban ƙaramar hukumar Ika da kuma dan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Abak ta tarayya.

Kara karanta wannan

Maganar N Power ta dawo, Tinubu ya umarci sake fasalinta, matasa za su caɓa

A cewar sanarwar, jajircewar ministan ga zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban Jihar Akwa Ibom ne ya sa yake haɗin kai da Gwamna Eno.

Ohanaeze ta amince Tinubu ya yi takwas

Kuna da labarin cewa ƙungiyar kabilar Ibo ta Ohanaeze Ndigbo ta bayyana cikakken goyon bayanta ga Shugaba Bola Tinubu ya yi tazarce zango na biyu a 2027.

Sai dai kungiyar ta roki mai girma shugaban ƙasa da ya yi amfani da karfin mulkinsa ya kawo ƙarshen ƙungiyar ƴan awaren IPOB a Kudu maso Gabas.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262