Ministan Tinubu Ya Fadi Yadda Ya Cire Tsohon Shugaban PDP daga Muƙaminsa

Ministan Tinubu Ya Fadi Yadda Ya Cire Tsohon Shugaban PDP daga Muƙaminsa

  • Ministan Abuja, ya bayyana dalilin da ya sa ya haɗa baki aka cire tsohon shugaban PDP, Prince Uche Secondus daga mukaminsa
  • Nyesom Wike ya fadi haka ne bayan Secondus ya ce suna daga cikin makiyansa a jihar Rivers wanda ya bata masa rai
  • Ya kuma bayyana cewa ya fi kowane gwamna a gwamnatin Bola Tinubu samar da damar aikin gwamnati ga mutanen jiharsa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Rivers - Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana dalilin da yasa ya goyi bayan cire tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Prince Uche Secondus.

Wike ya ce Secondus ya yi kokarin kakaba wa yan Rivers dan uwansa a matsayin gwamnan jihar.

Wike ya tona ashirin yadda aka cire tsohon shugaban PDP a Najeriya
Nyesom Wike ya ce ya haɗa baki an cire Uche Secondus daga muƙamin shugaban PDP saboda neman kakaba musu dan uwansa a matsayin gwamna. Hoto: Nyesom Ezenwo Wike, Sir Siminalayi Fubara.
Source: Facebook

'Secondus ya so kakaba mana dan uwansa' - Wike

Ministan ya bayyana hakan ne a yayin da yake jawabi a bikin godiya da PDP ta shirya a Ahoada ta Yamma, cewar Vanguard.

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP ya ziyarci Tinubu a Legas, an ji abin da suka tattauna a cikin bidiyo

Wike ya ce ya goyi bayan cire Secondus saboda ya shirya kakaba dan uwansa, Tele Ikuru, gwamna madadin Siminalayi Fubara.

A cewar Wike, Celestine Omehia ya yi kokarin zama gwamnan jihar Ribas ta bayan fage, amma an hana shi saboda rashin cancanta.

Ministan ya bayyana cewa babu wani gwamna a gwamnatin Bola Tinubu da ya samar da dama ga jiharsa kamar yadda ya yi wa Rivers, The Nation ta ruwaito.

Yadda Wike ya shirya cire Secondus a PDP

"Na kori Secondus a matsayin shugaban PDP lokacin da ya so mayar da dan uwansa, Tele Ikuru, gwamna."
"A yau kuma, yana cewa yanzu mu abokan gaba ne."
"Shi ne wanda ya hana mutumin zama gwamna, ya so dan uwansa ya zama gwamna."

- Nyesom Wike

Legit Hausa ta yi magana da dan PDP

Wani dan a mutum PDP, Kwamred Abubakar Abdulkadir ya ce Nyesom Wike yana kawo cikas ga jam'iyyar.

Kara karanta wannan

"An samu tsaro a 2024," Gwamnan a Arewa ya yabawa Shugaban Kasa Tinubu

"Duk wata matsalar PDP Wike yana da hannu a ciki yayin da yake cigaba da kasancewa a gwamnatin APC."
"Ya kamata jam'iyyar ta ɗauki matakin da ya dace kansa domin sanin makomarsa a cikinta."

- Kwamred Abdulkadir

Dan PDP ya shawarci masu ruwa da tsaki a jam'iyyar su nemo hanyar sulhu saboda shawo kan wadanda suka fandare.

Wike ya shirya tatsar biliyoyi daga filaye

Kun ji cewa Hukumar gudanarwar Abuja ta fara harin tara Naira biliyan 30 daga manyan kasar nan da kamfanoni da suka mallaki filaye.

A baya dai, Ministan Abuja, Nyesom Wike ya bayar da wa'adin mako biyu ga masu filayen da su biya kudaden da ake biyansu.

Ya bayyana hukuncin da aka shirya dauka matukar masu filaye da kamfanonin su ka yi biris da umarnin da hukuma ta ba su.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.