2027: Duk da Adawar Dattawa, Kungiyar Arewa Ta Goyi bayan Tazarcen Tinubu

2027: Duk da Adawar Dattawa, Kungiyar Arewa Ta Goyi bayan Tazarcen Tinubu

  • Kungiyar APC, reshen Arewa ta Tsakiya ta bayyana goyon bayanta ga shugaba Bola Tinubu domin tsayawa takara a zaben 2027
  • Wannan na zuwa ne yayin da kungiyoyin Arewa irinsu ACF da AYCF suka nuna rashin amincewarsu idan Tinubu zai zarce
  • Sai dai kungiyar APC reshen Arewa ta Tsakiya ta ce gyaran kasa, inganta tsaro da rabon mukamai sun isa a marawa Tinubu baya

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Kungiyar APC ta Arewa ta Tsakiya ta goyi bayan shugaba Bola Ahmed Tinubu domin ya sake tsayawa takara a 2027.

Kungiyar ta ce Tinubu ya samar da damarmaki masu yawan gaske ga shiyyar Arewa ta Tsakiya tun shigarsa ofis a ranar 29 ga Mayu, 2023.

Kungiyar APC, Arewa ta Tsakiya ta yi magana kan goyon bayan takarar Tinubu a 2027
Kungiyar APC a Arewa ta amince za ta goyi bayan Tinubu a zaben 2027. Hoto: @PBATMediaCentre
Source: Twitter

Kungiyar Arewa ta goyi bayan tazarcen Tinubu

Shugaban kungiyar, Alhaji Saleh Zazzaga, ya bayyana cewa yankin zai goyi bayan Tinubu a zaben shugaban kasa na 2027 da ke tafe, inji rahoton Daily Trust.

Kara karanta wannan

Tinubu: Wasu ƴan Arewa sun bayyana wanda za su marawa baya a 2027

A cikin wata sanarwa da ya fitar jim kadan bayan taron kungiyar a Abuja, Alhaji Saleh ya ce Arewa maso Gabas za ta rama halaccin da Tinubu ya yi mata a 2027.

Wannan na zuwa ne yayin da kungiyar Arewa Consultative Forum da matasanta (AYCF) suka nuna rashin goyon baya ga kudurin tazarcen Tinubu a zaben 2027.

A wata sanarwa, kungiyar ACF ta ce za ta goyi bayan dan Arewa ne kawai a zaben shugaban kasar Najeriya, duk da wannan zance ya jawo sabani a yankin.

Kungiyar APC ta juyawa ACF, AYCF baya

Shi ma shugaban kungiyar AYCF, Alhaji Shettima Yerima, ya ce yankin Arewa yana nadamar goyon bayan Tinubu a zaben 2023.

Kungiyar AYC ta gargadi Tinubu cewa Arewa ba za ta saurare shi a zaben 2027 ba ma muddin gwamnatinsa ba ta inganta tattalin arziki ba.

Sai dai, kungiyar APC, reshen Arewa ta Tsakiya ta ce yankinta ya ci gajiyar mulkin Tinubu ta fannin gyare-gyaren kasa, rabon mukamai da inganta tsaro.

Kara karanta wannan

Ana neman Obasanjo, IBB, Buhari, Jonathan su hadu, su kifar da Tinubu a 2027

Tsadar rayuwa: ACF ta taso Tinubu a gaba

A wani labarin, mun ruwaito cewa dattawan Arewa sun nuna damuwa kan matsin tattalin arziƙi a Najeriya, suna danganta hakan ga wasu manufofin Bola Tinubu.

Kungiyar dattawan ta ACF ta gargadi mahukunta da su gaggauta ɗaukar matakan magance matsalolin tattalin arziƙi domin gujewa ƙarin taɓarɓarewar halin rayuwa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com