Tsohon Kwamishinan Ganduje Ya Soki Sakacin APC a Kano, Ya Fadi Kuskuren da Ake Yi

Tsohon Kwamishinan Ganduje Ya Soki Sakacin APC a Kano, Ya Fadi Kuskuren da Ake Yi

  • Tsohon kwamishina a Kano, Mu'az Magaji ya caccaki tsarin yadda jam'iyyar APC ke neman mulki a jihar
  • Magaji ya ce kwata-kwata bai goyon bayan yadda jam'iyyar ke dogara da karfin gwamnati daga sama
  • Ya ce idan za ta sake lale kawai ta yi domin a fito a nemi al'umma a zabe da kuma mutunta yan jam'iyya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Yayin da ake cigaba da zaben kananan hukumomi a Kano, tsohon kwamishina, Mu'az Magaji ya ba jam'iyyar APC shawara

Tsohon kwamishinan ayyuka a mulkin Abdullahi Ganduje ya gargadi jam'iyyar kan cigaba da dogara da karfin Gwamnatin Tarayya.

Kara karanta wannan

Ana matsalar lantarki. 'yan Arewa sun dura kan Tinubu, sun ragargaje shi

Kusa a APC ya koka kan yadda jam'iyyar ke tafiyar da siyasar Kano
Tsohon kwamishina a mulkin APC ya caccaki yadda jam'iyyar ke gudanar da siyasarta a Kano. Hoto: Mu'az Magaji.
Asali: Facebook

Kusa a APC ya soki tsarinta a Kano

Mu'az Magaji ya bayyana haka ne a shafinsa na Facebook a yau Asabar 26 ga watan Oktoban 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Magaji ya ce kwata-kwata hanyar da APC ke bi a siyasar Kano kuskure ne dole ta sake lale domin dawo da martabarta.

Tsohon kwamishinan ya ce ya kamata APC ta nemi al'umma a zabe ba wai yanke hukuncin zaben daga sama ba.

Kano: Mu'az Magaji ya ba APC shawara

"Za mu tafka kuskure babba a APC idan mu ka cigaba da dogara da karfin Gwamnatinmu a sama don samun nasarar siyasa a Kano."
"Irin wannan ne yasa aka kada mu a 2023, siyasa daban gwamnati daban, sai mun sake lale a Kano."
"Ni bana goyon bayan a rika yanke hukuncin zabe da juya siyasar Kano daga sama, a bari kowa ya nemi mutane, a daraja yan jamiyya, a yi bayanin abinda za a aiwatar wa mutane har su amsa mana, mu karbe abinda suka karba da kyar."

Kara karanta wannan

Bayan Tinubu ya kori ministoci 5, ɗan takarar gwamna ya dawo jam'iyyar APC

- Mu'az Magaji

Babu jami'an tsaro a zaben Kano

Mun baku labarin cewa ana cigaba da gudanar da zaben kananan hukumomi a Kano ba tare da jami'an tsaro ba a mafi yawan wurare.

Mafi yawan mazabu babu jami'an tsaro sai dai yan banga rike da sanda da adduna da kuma yan KAROTA da ke kula da hanyoyi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.