Kano: Sarki Sanusi Ya Magantu kan Zaben Kananan Hukumomi, Ya Tura Muhimmancin Sako

Kano: Sarki Sanusi Ya Magantu kan Zaben Kananan Hukumomi, Ya Tura Muhimmancin Sako

  • Ana ƙoƙarin gudanar kananan hukumomi a Kano, Sarki Muhammadu Sanusi II ya ba da shawarwari ga iyaye
  • Sarki Muhammadu Sanusi ya shawarci iyaye da su kange ƴaƴansu daga shiga rigima yayin gudanar da zaben a jihar
  • Hakan ya biyo bayan shirye-shiryen gudanar da zaben kananan hukumomi a gobe Asabar 25 ga watan Oktoban 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya yi magana kan zaben kananan hukumomi.

Sarki Sanusi II ya shawarci iyayen yara da matasa da su ja kunnen 'ya'yansu kan shiga rikici yayin zaɓen a jihar Kano.

Sanusi II ya yi magana kan zaben kananan hukumomi a Kano
Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya ba Iyaye shawara kan zaben kananan hukumomi. Hoto: Sanusi Lamido Sanusi.
Asali: Twitter

Kananan hukumomi: Sanusi II ya shawarci iyaye

Kara karanta wannan

"Ban da APC:" KANSIEC ta fadi jam'iyyun da ke takara a zaben Kano

Vanguard ta tabbatar da cewa Sarkin ya fadi haka ne yayin ganawa da yan jaridu a yau Juma'a 25 ga watan Oktoban 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanusi II ya ce duk mai kaunar jihar Kano zai so a ce ta zauna lafiya ba tare da neman tashin hankali ba, cewar rahoton Punch.

"Ga mutane na yan jihar Kano, kamar yadda kuka sani a gobe Asabar za a gudanar da zaben kananan hukumomi."

- Muhammadu Sanusi II

Sarki Sanusi ya tura sako ga limamai

"Duk wadanda suke son Kano, ina da tabbacin cewa za su yarda da ni cewa babu abin da yafi zaman lafiya muhimmanci."
"Wadanda ke kawo rigima a Kano mafi yawansu makiyanta ne, za su ta da rigima kuma a ta kashe kannenmu da 'ya'yanmu."
"Ina kira ga iyaye da masu unguwanni da hakimai da kuma limamai da su ja kunnen matasa kan ta da rigima."

Kara karanta wannan

Kotu ta yanke hukunci kasa da awanni 24 kafin zaben Ciyamomi a jihar Kano

- Sarki Muhammadu Sanusi II

Babu APC a zaben kananan hukumomin Kano

Kun ji cewa Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kano ta ce dama a shirye ta ke wajen gudunar da zaben ciyamomi ba tare da cikas ba.

Shugaban hukumar, Farfesa Sani Malumfashi ya fadi haka jim kaɗan bayan hukuncin babbar kotun jiha da ya sahale a yi zabe.

Farfesa Sani Malumfashi ya ce amma babbar jam'iyyar adawa ta APC ta fice daga zaben duk da zama da aka yi da ita.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.