Tinubu, Ganduje Sun Yi Kicibis da Atiku da Manyan Yan Adawarsa a Siyasa, Bayanai Sun Fito

Tinubu, Ganduje Sun Yi Kicibis da Atiku da Manyan Yan Adawarsa a Siyasa, Bayanai Sun Fito

  • An yi kicibis bayan Shugaba Bola Tinubu ya hadu da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar
  • Shugaba Tinubu ya ci karo da babban mai masa adawa a siyasa wanda ya yi takara da shi a zaben 2023 da ta gabata
  • Shugaban kasar ya hadu da Atiku ne a babban masallacin birnin Tarayya da ke Abuja yayin sallar Juma'a a yau

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya ci karo da manyan yan adawansa a birnin Abuja.

Bola Tinubu ya yi kicibis da dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar a masallacin Juma'a.

Tinubu ya hadu da babban dan adawansa, Atiku Abubakar a Abuja
Shugaba Bola Tinubu ya hadu da tsohon dan takarar PDP, Atiku Abubakar. Hoto: Taiwo Okonlawon.
Asali: Twitter

Atiku ya ci karo da Tinubu a masallacin Juma'a

Kara karanta wannan

Nadin Minista ya jefa Tinubu a matsala, APC ta zarge shi da cin amanar jam'iyya

NTA News ta wallafa wani hoto da aka dauka bayan sallar Juma'a da aka gudanar a babban masallacin Abuja.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin hoton, an gano shugaban jam'iyyar APC, Dakta Abdullahi Umar Ganduje yana rike da Alkur'ani mai girma a gefe.

Daga cikin wadanda suke tare a cikin masallacin akwai Gwama Bala Mohammed na jihar Bauchi wanda yake yawan sukar gwamnatin Tinubu.

Har ila yau, a can gefe, akwai tsohon gwamnan Borno kuma jigon jam'iyyar APC, Sanata Ali Modu Sherrif.

Karanta wasu labarai game da Atiku da Tinubu

Kara karanta wannan

Jerin ministocin da Tinubu ya kora daga aiki da jihohin da suka fito a Najeriya

Atiku ya soki tsarin mulkin Bola Tinubu

Kun ji cewa Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin Bola Tinubu saboda matakin da ta dauka kan NLC.

Atiku Abubakar ya ce yadda gwamnatin kasar nan ke kokarin murkushe kungiyoyin kwadago na nuna tsagwaron zalunci.

Tsohon dan takarar shugaban kasar ya kuma buga misali da yadda aka kama wani dan jarida, bayan an sake shi aka ce kuskure ne.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.