Jerin Ministocin da Tinubu Ya Kora daga Aiki da Jihohin da Suka Fito a Najeriya

Jerin Ministocin da Tinubu Ya Kora daga Aiki da Jihohin da Suka Fito a Najeriya

  • Ministoci 5 ne suka rasa muƙamansu da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi garambawul a majalisar zartaswa ranar Laraba
  • Shugaba Tinubu ya ɗauki matakin korar ministocin ne bayan taron majalisar zartaswa FEC a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja
  • Hakan dai wani ɓangare ne a yunƙurin shugaban kasar na yi wa ma'aikatu kwaskwarima a gwamnatinsa bayan kusan shekara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

State House, Abuja - A jiya Laraba ne shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya sallami ministoci biyar daga aiki.

Kafin haka Shugaba Tinubu ya sanar da rusa ma'aikatar raya yankin Neja Delta da ma'aikatar kula da harkokin wasanni duk a ƙoƙarin yin garambawul.

Kara karanta wannan

Jerin kananan Ministoci da suka koma manya bayan Tinubu ya yi garambawul

Tahir Mamman, Bola Tinubu da Uju-Ken Ohanenye.
Jihohin da korarrun ministocin Tinubu suka fito a Najeriya Hoto: @DeeOneAyekooto
Asali: Twitter

Hadimin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a shafin X, inda ya ce Tinubu ya kirkiro ma'aikatar ci gaban yankuna da za ta kula da harkokin Neja Delta da sauran yankuna.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya kuma sauke ministoci biyar bayan taron majalisar zartaswa ta ƙasa watau FEC a Abuja ranar Laraba, 23 ga watan Oktoba, 2024.

Ministar harkokin mata, Barista Uju-Ken Ohanenye, da Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman su ne manya daga cikin waɗanda aka kora daga aiki.

Ministocin da Tinubu ya sauke da jihohinsu

1. Ministar harkokin mata, Barista Uju-Ken Ohanenye (jihar Anambra).

2. Ministan ilimi, Farfesa Tahir Mamman (jihar Adamawa).

3. Ministar harkokin yawon buɗe ido, Lola Ade-John (jihar Ekiti)

4. Ƙaramin Ministan gidaje ɗa raya birane, Abdullahi Muhammad Gwarzo (jihar Kano).

5. Ministar harkokin ci gaban matasa, Jamila Bio Ibrahim (jihar Kwara).

Kara karanta wannan

A ƙarshe, Bola Tinubu ya maye gurbin Betta Edu, ya naɗa sabon ministan jin ƙai

A karshe, Shugaɓa Tinubu ya masu fatan alheri da godiya bisa aikin da suka yi wa ƙasa a tsawon lokacin da suka ɗauka kan muƙamansu.

Bola Tinubu ya maye gurbin Betta Edu

A wani rahoton kuma shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Betta Edu, dakatacciyar ministar harkokin jin ƙai da yaye talauci.

Shugaban ƙasar ya naɗa Dr Nentawe Yilwatda a matsayin sabon ministan jin ƙai, wanda zai maye gurbin Betta Edo bayan dogon lokaci da dakatar da ita.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262