Ta Faru Ta Kare, Kotu Ta Tsige Shugaba da manyan Jami'an Hukumar Zaben Jihar Kano

Ta Faru Ta Kare, Kotu Ta Tsige Shugaba da manyan Jami'an Hukumar Zaben Jihar Kano

  • Wata babbar kotun tarayya ta kori shugaban hukumar zaben jihar Kano, Farfesa Sani Malumfashi daga kan kujerarsa
  • Hakazalika, kotun ta kori wasu daga cikin manyan jami'an hukumar zaben saboda kasancewarsu 'yan jami'iyyar NNPP
  • Babbar kotun ta kuma haramtawa KANSIEC gudanar da zaben kananan hukumomin jihar har sai an nada sababbin shugabanni

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta tsige shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano (KANSIEC), Farfesa Sani Malumfashi.

A hukuncin da ta yanke a ranar Talata, kotun ta tsige Farfesa Malumfashi saboda kasancewarsa dan jam’iyyar NNPP a hukumance.

Kotu ta yi hukunci kan cancantar shugabannin hukumar zaben jihar Kano
Kotu ta tsige shugaban hukumar zaben jihar Kano saboda kasancewarsa dan NNPP. Hoto: Bashir Habib Yahya
Asali: Facebook

Aminu Tiga da jam’iyyar APC ne suka shigar da karar, kamar yadda rahoton jaridar The Nation ya nuna.

Kara karanta wannan

Taron NEC: Rikicin PDP ya ɗauki sabon salo, gwamna ya jagoranci kai ƙara kotu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotu ta yi hukunci kan karar APC

Wadanda ake karar dai sun hada da babban lauyan gwamnati kuma kwamishinan shari’a na jihar, Haruna Dederi da wasu mutum 14.

Da yake yanke hukunci, Mai shari’a S.A Amobede, ya kuma ce Kabir Zakirai, sakataren hukumar ba ma’aikacin gwamnatin jihar Kano ba ne.

Alkalin kotun ya ce Zakirai bai cancanci a nada shi mukamin ba kamar yadda sashi na 14 na dokar hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano ta shekarar 2001 ta tanada.

“An rusa duk abin da wanda ake tuhuma na takwas ke yi a shirye-shiryen zaben kananan hukumomin jihar Kano a shekarar 2024 kuma shirin ba shi da wani tasiri."

- A cewar kotun.

Kano: An tsige shugabannin KANSIEC

Mai shari'a S.A Amobede ya ci gaba da cewa:

"Da wannan, kotu ta rusa nadin wadanda ake kara na 8 zuwa na 14 ba tare da bata lokaci ba kuma an kore su daga mukamansu na shugaba da jami'an hukumar.

Kara karanta wannan

Kotun Koli za ta yi hukunci kan bukatar rusa EFCC da gwamnoni 16 suka shigar

“An hana su gudanar da zaben kananan hukumomi 44 na jihar Kano da aka shirya yi a 2024 har sai an nada wadanda suka cancanta."

Ya kuma umurci ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su gaggauta tabbatar da cika sharuddan sashe na 197 (1) (b) da 199 (2) da 200 (1) (a) na kundin tsarin mulkin Najeriya.

Kotu ta hana zaben ciyamomin Kano

Tun da fari, mun ruwaito cewa wata babbar kotun tarayya ta dakatar da hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Kano daga gudanar da zaben ƙananan hukumomi.

Mai shari’a S.A Amobede ya yanke hukuncin cewa nada Farfesa Sani Malumfashi matsayin shugaban hukumar zaben alhalin yana cikin jam'iyyar NNPP ya saba doka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.