Babbar Kotu Ta Yanke Hukunci kan Zaben Kananan Hukumomin da Za a Yi a Kano

Babbar Kotu Ta Yanke Hukunci kan Zaben Kananan Hukumomin da Za a Yi a Kano

  • Babbar kotun tarayya ta hana zaɓen ƙananan hukumomin da ake shirin yi a Kano ranar Asabar, 26 ga watan Oktoba, 2024
  • Alkalin kotun, Mai Shari'a Simon Ameboda ya ce naɗn ƴan jam'iyyar NNPP a matsayin shugabannin hukumar zaɓen Kano ya saɓa doka
  • Ya kuma umarci hukumar zaɓe ta ƙasa watau INEC kada ta ba Kano kayan zaɓe har sai an gyara naɗe-naɗen hukumar KANSIEC

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Babbar kotun tarayya mai zama a Kano ta hana gudanar da zaɓen kananan hukumomin da aka shirya yi ranar Asabar mai zuwa.

Alkalin kotun Mai Shari'a Simon Ameboda ne ya yanke wannan hukuncin a zaman yau Talata, 22 ga watan Oktoba, 2024.

Kara karanta wannan

Mutane sun shiga matsala yayin da ruwa ya mamaye garuruwa 25, an samu bayanai

Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Kotu ta hana zaben kananan hukumomin jihar Kano ranar Asabar mai zuwa Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Facebook

Meyasa ƙotu ta hana zaɓen Kano?

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, alkalin ya ce naɗin shugaban hukumar zaɓen Kano da sauran ƴan kwamitin gudanarwa ya saɓa tanadin kundin tsarin mulki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mai shari'a Ameboda ya ce naɗin ƴan jam'iyyar NNPP a matsayin waɗanda za su tafiyar da hukumar KANSIEC ya saɓawa dokar sashi na 197(1) da sahi na 200(1) na kundin tsarin mulki na 1999.

Haka na kuma ya saɓawa dokar dashi na 4(b) na kundin dokokin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano 2001.

Kotu ta hana INEC ba da kayan zaɓe

Kotun ta bayyana cewa a yadda hukumar KANSIEC gake a halin yanzu, ba za ta iya gudanar da sahihin zaɓen kananan hukumomi ba a Kano, rahoton Guardian.

Bugu da ƙari, babbar kotun tarayya ta umarci hukumar zaɓe mai zman kanta INEC da kada ta ba KANSIEC kayayyki zaɓe har sai an gyara shugabancinta.

Kara karanta wannan

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ya gindaya sharadin haɗa kai a zaben 2027

Hukumar KANSIEC dai ta shirya gudanar da zaɓen ciyamomi da kansiloli a faɗin kananam hukumomi 44 da ke Kano ranar Asabar, 26 ga watan Oktoba.

NNPP ta ƙara rasa jiga-jiganta a Kano

A wani rahoton kuma jam'iyyar NNPP ta sake samun koma baya a jihar Kano bayan wasu jagororinta sun sauya sheƙa zuwa APC mai adawa a Kano

Jagororin jam'iyyar NNPP da suka sauya sheƙa zuwa APC sun fito ne dagaa ƙananan hukumomin Tofa da Dawakin Tofa na Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262