"Ka da Zaben Edo Ya Rude Ka": PDP Ta Ja Kunnen Ganduje kan Kwace Jihohin Yarbawa

"Ka da Zaben Edo Ya Rude Ka": PDP Ta Ja Kunnen Ganduje kan Kwace Jihohin Yarbawa

  • Ana shirin zaben Ondo, jam'iyyar PDP ta ja kunnen shugaban APC, Abdullahi Ganduje kan zaben da za a yi a Nuwamba
  • Jam'iyyar PDP ta gargadi Ganduje kan kalamansa da ya ce za su kwace dukan jihohin Kudu maso Yamma a Najeriya
  • PDP ta ja kunnen Ganduje da ya yi hankali da yankin saboda sun waye a siyasa ba kamar Edo ba ne da za a siye su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Jam'iyyar PDP ta mayar da martani ga Abdullahi Ganduje kan kwace yankin Kudu maso Yamma.

Jam'iyyar PDP ta ce yankin Kudu maso Yamma ba kamar jihar Edo ba ne inda ya ce ka da zaben Edo ya yaudare su.

Kara karanta wannan

'Ana shan wuya,' Wani babba a APC ya cire kunya ya koka kan mulkin Tinubu

Jam'iyyar PDP ta caccaki shugaban APC, Ganduje
Jam'iyyar PDP ta gargadi Ganduje kan kalamansa na kwace yankin Kudu maso Yamma. Hoto: Peoples Democratic Party, PDP, All Progressives Congress.
Asali: Facebook

Ganduje ya sha alwashin kwace yankin Yarbawa

Sakataren jam'iyyar, Debo Ologunagba shi ya tura wannan gargadi a jiya Litinin 21 ga watan Oktoban 2024, cewar rahoton Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ologunagba ya ce yankin Kudu maso Yamma ba kamar Edo ba ne da za a kwace ko siya a zabe kamar yadda APC ke yi.

Wannan martani na zuwa ne bayan Ganduje ya sha alwashin cewa APC za ta kwace duka jihohin yankin guda shida.

Ganduje ya fadi haka ne a birnin Akure da ke jihar Ondo a ranar Lahadi 20 ga watan Oktoban 2024 yayin jawabinsa.

Jam'iyyar APC na rike da jihohin Lagos da Ekiti da Ondo da kuma Ogun inda PDP ke jagorancin Oyo da Osun.

PDP ta ja kunnen Ganduje kan zaben Ondo

Sai dai jam'iyyar PDP ta yi martani ga Ganduje inda ta ce kalamansa shiririta ne kawai da rashin tsari, cewar Vanguard.

Kara karanta wannan

“Nan ba Legas ko Edo ba ce:” NNPP ta yi kurarin samun nasara a zaben Gwamna

"Wannan gargadi ne, mutanen yankin Kudu maso Yamma wayayyu ne a siyasa sun san abin da suke so."
"Kamar yadda Ganduje ya je Ondo ya ke fadan abin ba su dace ba, wannan barazana ne ga dimukraɗiyya."
"Ya kamata ya yi hankali da yankin, zaben Ondo ba irin wanda ya saɓa gani ba ne, yan jihar sun shirya tsaf domin zaben PDP."

- Debo Ologunagba

Ganduje ya musanta shirin neman kujerar Tinubu

Kun ji cewa Shugaban APC Abdullahi Ganduje ya musanta raɗe-raɗin yana shirin tsayawa takarar shugaban ƙasa a babban zaɓen 2027.

Ganduje ya ce fastocin da ke yawo a Abuja ba su da alaƙa da shi kuma ya yi zargin akwai hannun wasu ƴan Kwankwasiyya a ciki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.