Kananan Hukumomi: Yan Sanda Sun Tarwatsa Matasa, An Fadi halin da Ake Ciki a Kaduna

Kananan Hukumomi: Yan Sanda Sun Tarwatsa Matasa, An Fadi halin da Ake Ciki a Kaduna

  • Yan sanda sun tarwatsa wasu matasa da ke kokarin kawo cikas a zabukan kananan hukumomi da ake cigaba da yi
  • Jami'an tsaro sun jefa barkonon tsohuwa kan matasan da ke neman ta da rigima a ofishin hukumar zaben jihar da ke Gwantu
  • Hakan ya biyo bayan cigaba da zaben kananan hukumomi a jihar Kaduna da ake yi a yau Asabar 19 ga watan Oktoban 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kaduna - Yayin da ake cigaba da zaben kananan hukumomi a jihar Kaduna, an fara samun matsala.

Wasu matasa sun durfafi ofishin hukumar zaben jihar, KADSIECOM a yau Asabar 19 ga watan Oktoban 2024.

Kara karanta wannan

Katsina: Yan bindiga sun sace shugaban jam'iyyar APC, sun kashe jami'in tsaro

An watsa matasa da ke kokarin tada kayar baya a Kaduna
Yan sanda sun watsawa matasa da ke neman tada rigima a Kaduna barkonon tsohuwa. Hoto: Uba Sani.
Asali: Twitter

Yan sanda sun watsa matasa a Kaduna

Yan sanda sun tarwatsa matasan da ke faman tada rigima a ofishin hukumar zaben jihar, kamar yadda Aminiya ta wallafa bidiyo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Lamarin ya faru ne a ofishin hukumar zaben jihar da ke garin Gwantu a jihar Kaduna da ke Arewa maso Yamma.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an samu tsaiko a wurare da dama da ake gudanar da zabukan a yau Asabar 19 ga watan Oktoban 2024.

Mafi yawan wuraren da aka samu cikas ya faru ne saboda rashin zuwan jami'an hukumar a kan lokaci.

Karanta labarai game da zabukan kananan hukumomi

Kara karanta wannan

Sojoji sun gano gidan da yan bindiga ke boye makamai, an kama mata da miji

Kananan hukumomi: Halin da ake ciki a Kaduna

Kun ji cewa Mutane a birnin Kaduna sun yi biris da dokar hana zirga-zirga da gwamnatin jihar ta sanya domin zaɓen ƙananan hukumomin jihar.

Masu ababen hawa sun ci gaba da gudanar da harkokinsu duk kuwa da dokar hana zirga-zirgar da aka sanya a ranar Asabar, 19 ga watan Oktoba 2024 .

Tun da farko dai gwamnatin jihar ta sanya dokar hana zirga-zirgar daga ƙarfe 6:00 na safe zuwa ƙarfe 7:00 na Yamma.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.