Kananan Hukumomi: Yan Sanda Sun Tarwatsa Matasa, An Fadi halin da Ake Ciki a Kaduna

Kananan Hukumomi: Yan Sanda Sun Tarwatsa Matasa, An Fadi halin da Ake Ciki a Kaduna

  • Yan sanda sun tarwatsa wasu matasa da ke kokarin kawo cikas a zabukan kananan hukumomi da ake cigaba da yi
  • Jami'an tsaro sun jefa barkonon tsohuwa kan matasan da ke neman ta da rigima a ofishin hukumar zaben jihar da ke Gwantu
  • Hakan ya biyo bayan cigaba da zaben kananan hukumomi a jihar Kaduna da ake yi a yau Asabar 19 ga watan Oktoban 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kaduna - Yayin da ake cigaba da zaben kananan hukumomi a jihar Kaduna, an fara samun matsala.

Wasu matasa sun durfafi ofishin hukumar zaben jihar, KADSIECOM a yau Asabar 19 ga watan Oktoban 2024.

An watsa matasa da ke kokarin tada kayar baya a Kaduna
Yan sanda sun watsawa matasa da ke neman tada rigima a Kaduna barkonon tsohuwa. Hoto: Uba Sani.
Source: Twitter

Yan sanda sun watsa matasa a Kaduna

Kara karanta wannan

Kogi: An sanar da sakamakon zaben kananan hukumomi, mace tilo ta samu kujera

Yan sanda sun tarwatsa matasan da ke faman tada rigima a ofishin hukumar zaben jihar, kamar yadda Aminiya ta wallafa bidiyo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Lamarin ya faru ne a ofishin hukumar zaben jihar da ke garin Gwantu a jihar Kaduna da ke Arewa maso Yamma.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an samu tsaiko a wurare da dama da ake gudanar da zabukan a yau Asabar 19 ga watan Oktoban 2024.

Mafi yawan wuraren da aka samu cikas ya faru ne saboda rashin zuwan jami'an hukumar a kan lokaci.

Karanta labarai game da zabukan kananan hukumomi

Kananan hukumomi: Halin da ake ciki a Kaduna

Kun ji cewa Mutane a birnin Kaduna sun yi biris da dokar hana zirga-zirga da gwamnatin jihar ta sanya domin zaɓen ƙananan hukumomin jihar.

Kara karanta wannan

Sunayen wadanda za su zama sababbin shugabannin kananan hukumomin Kaduna

Masu ababen hawa sun ci gaba da gudanar da harkokinsu duk kuwa da dokar hana zirga-zirgar da aka sanya a ranar Asabar, 19 ga watan Oktoba 2024 .

Tun da farko dai gwamnatin jihar ta sanya dokar hana zirga-zirgar daga ƙarfe 6:00 na safe zuwa ƙarfe 7:00 na Yamma.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.