Tsohon Gwamna a Arewa Ya Feɗe Gaskiya kan Rigimar Shugabancin PDP na Ƙasa

Tsohon Gwamna a Arewa Ya Feɗe Gaskiya kan Rigimar Shugabancin PDP na Ƙasa

  • Samuel Ortom ya bayyana cewa babu wani ɓangare a jam'iyyar PDP ta kasa kamar yadda ake yaɗawa a baya-bayan nan
  • Tsohon gwamnan jihar Benuwai ya ce Umar Damagum ne sahihin shugaban PDP na riko, babu wani tsagi da ya ɓalle
  • Wannan na zuwa ne a lokacin da rigimar cikin gida ke ƙara kamari a babbar jam'iyyar adawa bayan wani tsagi ya naɗa Yayari Mohammed

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Benue - Tsohon gwamnan jihar Benuwai, Samuel.Ortom ya ce babu wani ɓangare na daban a PDP saɓanin yadda ake yaɗawa cewa jam'iyyar ta dare gida biyu.

Ortom, ɗaya daga cikin gwamnonin biyar da suka kafa tawagar G5 a kakar zaɓen 2023 ya ce Umar Damagum ne kaɗai sahihin shugaban PDP na ƙasa.

Kara karanta wannan

Gwamna Abba ya shirya ɗaukar sababbin ma'aikata sama da 17,000 a Kano, bayanai sun fito

Samuel Ortom.
Ortom ya ce babu wani bangare a jam'iyyar PDP ta ƙasa Hoto: Samuel Ortom
Asali: Twitter

A cewarsa, duk wani kwamitin gudanarwa watau NWC da ba Damagum ke jagoranta ba, ba shi da alaƙa da babbar jam'iyyar adawa, Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ortom ya yabi NWC karƙashin Damagum

Tsohon gwamnan ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya karɓi bakuncin sababbin ƴan kwamitin gudanarwa na jihar Benuwai a gidansa na Makurɗi.

Ya ƙara da cewa NWC karkashin Damagum ya yi iyakar bakin ƙakarinsa duk da rigingimin cikin gida da suka addabi jam'iyyar PDP.

Samuel Ortom ya ce maimakon a durkusar da shugabannin jam'iyyar, kamata ya yi a tallafa musu da yi musu addu’a, in ji Tribune Nigeria.

Da gaske PDP ta rabe gida biyu?

"Babu wani ɓangare a PDP, muna nan a layin da aka san mu na kokarin tabbatar da adalci, gaskia da daidaito, ban gusa daga nan ba, ni mai biyayya ne ga jam'iyya.

Kara karanta wannan

NNPP: Jam'iyyar Kwankwaso ta buɗe ƙofa, za a yi wa Tinubu taron dangi a 2027

"Ba mu son shiga cikin tawagar ƴan tawaye saboda haka muna tare da Damagum, yana bakin koƙarinsa, mun san babu ma'asumi kowa na iya yin kuskure.
"Kamata ya yi a yabawa yan kwamitin NWC karkashin Damagum maimakon a zauna ana zaginsu, sun yi ƙoƙari duk da kalubalen rigimar cikin gida."

- Samuel Ortom.

Makinde ya yi magana kan takara a 2027

A wani rahoton kuma gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde ya yi magana kan jita- jitar neman shugabancin kasa a zaɓen 2027.

Makinde ya ce shi mutum ne cikakke da ke da hankali wanda zai iya magana kan abubuwan da suka shafe shi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262