"Na Cancanta," Sanatan APC Ya Bayyana Shirinsa Na Neman Zama Shugaban Ƙasa a 2027

"Na Cancanta," Sanatan APC Ya Bayyana Shirinsa Na Neman Zama Shugaban Ƙasa a 2027

  • Sanata Orji Kalu ya bayyana cewa yana da gogewar zama shugaban kasa idan jam'iyyar APC ta ba shi dama a 2027
  • Kalu, tsohon gwamnan jihar Abia ya ce a shirye yake ya nemi takara a 2027 idan Bola Tinubu ya haƙura da tazarce
  • Sai dai sanatan mai wakiltar Arewacin Abia ya ce lissafinsa shi ne dawowa majalisar dattawa amma idan ya samu dama zai nemi kujera lamba ɗaya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Tsohon gwamnan Abia kuma Sanata mai wakiltar Abia ta Arewa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa ya cancanci zama shugaban kasa a 2027.

Sanata Kalu ya bayyana cewa zai nemi zama shugaban a 2027 idan har shugaba Bola Ahmed Tinubu bai nemi tazarce ba.

Kara karanta wannan

Gwamna a Arewa ya juyawa Tinubu baya, ya ce manufofinsa ne suka kawo yunwa

Sanata Orji Kalu.
Tsohon gwamnan Abia, Sanata Orji Kalu ya ce ya shirye yake ya karbi mulkin Najeriya Hoto: Senator Orji Kalu
Asali: Facebook

Orji Kalu ya yi wannan furucin ne ranar Alhamis a wata hira da gidan talabijin na Channels cikin shirinsu na siyasa a yau.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Zan iya mulkin Najeriya" - Kalu

"Bari na faɗa muku ni nan na cancanci zama shugaban Najeriya, inda gogewa da kwarewar da ake bukata to amma muna da ɗan takara a jam'iyyarmu ta APC sai dai idan ya haƙura.
"Idan kuma jam'iyyarmu ta ba ni dama, ta miƙa mun tikitin takarar shugaban ƙasa, ta karrama ni, ba wani abu ba ne da zan tsaya tunani domin ba ni kaɗai ya shafa ba, dama ce na samu.
"Sai dai ni a lissafi na majalisar dattawa zan sake dawowa a 2027 na kara yiwa ƙasata hidima."

- Orji Uzor Kalu.

Abin da ya kawo matsi a Najeriya

Da yake tsokaci kan halin matsin da ƙasar nan ke ciki, tsohon gwamnan ya ce ba komai ya jawo ma Najeriya haka ba sai rashin ingantaccen tsarin tattalin arziki.

Kara karanta wannan

"Allah ji ƙansu," Gwamnan Abba ya yi maganar mutuwar sama da mutum 100 a Jigawa

Sanata Kalu na APC ya ce a ra'ayinsa ya kamata gwamnati ta rage kashe-kashen kuɗi barkatai, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Ya ce shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na iya bakin ƙoƙarinsa wajen dawo da komai kan hanya amma ta yiwu a matsayin na ɗan adam ya yi kuskure a wani wurin.

Jigo ya nemi Kwankwaso, Atiku ta taimaka

A wani rahoton kuma tsohon kwamishina a Kano ya bayyana irin gudummuwar da ake bukata daga Rabiu Kwankwaso, Atiku Abubakar da Peter Obi.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya ce lokaci ya yi da manyan ƴan siyasar za su jingine adawa, su taimaki ƴan Najeriya a halin da ake ciki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262