Gwamnan Zamfara Ya Fadi Lokacin Gudanar da Zaben Ciyamomi

Gwamnan Zamfara Ya Fadi Lokacin Gudanar da Zaben Ciyamomi

  • Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a gudanar da zaben kananan hukumomi
  • Dauda ya bayyana cewa za a gudanar da zaɓen ne domin bin umarnin hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke kan cin gashin kansu
  • Ya kuma bayyana cewa hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar za ta fitar da jadawalin yadda zaɓen zai kasance

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Zamfara - Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomi.

Gwamna Dauda ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin wani taron majalisar zartarwa na jihar, inda ya jaddada muhimmancin gudanar da zaɓen kananan hukumomin bisa ga hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke.

Kara karanta wannan

Soke hukumar EFCC: Gwamna ya saba da takwarorinsa, ya ba da shawara

Gwamna Dauda ya fadi lokacin zabe a Zamfara
Gwamna Dauda ya ce za a yi zaben ciyamomi a Zamfara Hoto: Dauda Lawal
Asali: Twitter

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a shafinsa na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dauda ya rantsar da shugaban hukumar zaɓe

A taron majalisar, Gwamna Dauda Lawal ya kuma rantsar da Bala Aliyu Gusau a matsayin shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Zamfara.

Wa’adin masu kula da shugabancin ƙananan hukumomin jihar 14 zai ƙare ne a ranar 23 ga watan Oktoba, 2024.

Gwamna Dauda Lawal ya ƙara da cewa a kwanakin baya ya rattaɓa hannu kan gyaran dokar zaɓen jihar Zamfara, wacce ta shafi zaɓen ƙananan hukumomi da ke tafe.

Za a yi zaɓen ciyamomi a Zamfara

"Bisa hukuncin Kotun Ƙoli na baya-bayan nan, muna buƙatar mu gudanar da zaɓe a ƙananan hukumomin mu."
"Bayan rattaɓa hannu kan dokar da aka yi wa kwaskwarima, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jiha za ta sanar da jadawalin zaɓen da wuri-wuri domin mu samu zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomi a Zamfara."

Kara karanta wannan

Rashin tsaro: Gwamnan Zamfara ya fadi halin da ake ciki

- Gwamna Dauda Lawal

PDP ta lallasa APC a zaɓen ciyamomi

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar PDP ta samu gagarumar nasara kan APC da sauran jam'iyyun adawa a zaben kananan hukumomin jihar Filato.

Jam’iyyar PDP ta samu nasarar lashe kujerun kananan hukumomi 10 yayin da hukumar zaben Filato (PSIEC) ta fara bayyana sakamakon zaben.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng