Filato: Jama'a Sun Fusata yayin da INEC ke Neman Jami'ai Ranar Zabe

Filato: Jama'a Sun Fusata yayin da INEC ke Neman Jami'ai Ranar Zabe

  • Masu kada kuri'a a jihar Filato ba su samu yadda su ke so ba bayan an samu wasu matsaloli a tsarin gudanar da zaben
  • Rahotanni sun gano cewa an samu tsaiko saboda kin zuwan jami'an zaben INEC na wucin gadi wasu daga cikin mazauna
  • Lamarin ya sa masu zabe daga wasu mazabun sun sauya wurin kada kuri'a zuwa kananan hukumomin da ke kusa da su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Plateau – Masu kada kuri’a a jihar Filato sun bayyana rashin jin dadinsu kan yadda zaben kananan hukumomi ke gudana.

An samu rahoton rashin fara tantance masu zabe da wuri a wasu daga cikin mazabun da ke jihar.

Kara karanta wannan

"A kashe mu a huta:" Yan Najeriya sun koka da karin farashin litar man fetur

Plateau
Jami'an zabe ba su halarci wasu mazabu a Filato ba Biyo: Legit.ng
Asali: Original

A labarin da ya kebanta ga The Nation, an gano cewa an samu matsalar halartar jami'an zabe a wasu daga cikin kananan hukumomin Filato.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ba jami’an INEC a zaben Filato

Rahotanni sun bayyana cewa an samu rashin halartar jami’an zabe na wucin gadi daga hukumar INEC a karamar hukumar Jos ta Arewa.

Lamarin ya jawo rashin jin dadin masu kada kuri’a a wasu mazabun da ke kananan hukumomin Jos ta Arewa da Jos ta Gabas.

Filato: An samu lattin kayan zabe

Rahotanni sun tabbatar da cewa kayan zabe ba su isa wasu mazabu a jihar Filato da wuri ba duk da jama'a sun fito tun da sanyin safiya. A wasu wuraren, an samu jinkirin kayan gudanar da zaben har zuwa 11.00 na safe, yayin da masu zabe su ka hallara kusan 7.30 na safe.

Kara karanta wannan

Abubuwa 3 da suka jawo karamar jami'yya ta buga APC da PDP a kasa a Rivers

An kuma gano hukumar INEC na kokarin maye gurbin jami'an da ba ta da su a lokacin gudanar da zaben.

APC ta yi zarra a zaben Binuwai

A wani labarin kun ji cewa jam'iyyar APC ta doke dukkanin jam'iyyu wajen yin nasara a zaben kananan hukumomi 23 da ya gudana a jihar.

Shugaban hukumar zabe, Richard Tombowua ya bayyana nasarar da yan takarar APC su ka samu a zaben, sannan ya ce kansilolin jam'iyyar 276 sun yi nasara.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.