'Zancen Bur Inji Tusa', APC Ta Fadi Abin da Zai Faru a Hadakar Kwankwaso da Peter Obi
- Yayin da ake shirin haɗaka tsakanin Sanata Rabiu Kwankwaso da Peter Obi, jam'iyyar APC ta yi tsokaci kan lamarin
- Jam'iyyar ta ce babu wani abin tsoro a gare ta saboda dukansu yan son rai ne babu mai amincewa da haka
- Hakan ya biyo bayan jita-jitar cewa Kwankwaso ya amince da tayin zama mataimakin Peter Obi amma kan wasu sharuda
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
FCT, Abuja - Jam'iyyar APC ta yi martani game da shirin haɗaka tsakanin jam'iyyar NNPP da kuma LP.
APC ta ce ko a jikinta ba ta damu da shirin haɗaka tsakanin Sanata Rabiu Kwankwaso da Peter Obi na jam'iyyar LP ba.

Asali: Facebook
APC ta soki haɗakar Kwankwaso da Obi
Daraktan yada labaran jam'iyyar ta kasa, Bala Ibrahim shi ya bayyana haka yayin hira da jaridar Punch.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ibrahim ya ce wannan shiri babu inda zai je saboda an gwada yin haka a zaben 2023 da ya gabata.
Ya ce son rai da rashin yadda shi zai fara hada su fada saboda babu wanda zai sadaukar da neman takararsa ga wani.
Haɗakar NNPP-LP: APC ta fadi abin da zai faru
"Babban abin da zai wargaza wannan tafiya bai wuce rashin yadda a tsakaninsu ba wanda shi ne zai kawo cikas."
"Babu yadda za su yi nasara har sai idan akwai yadda a tsakaninsu wanda an gwada a baya ba a yi nasara ba."
"Da Kwankwaso da Obi sun sake shirin haɗaka wanda suka yi a baya da bai yi tasiri ba, dukansu suna da burin zama shugaban kasa babu mai sadaukar da haka ga dan uwansa."
- Bala Ibrahim
Ibrahim ya ce ko kadan hakan ba zai damu jam'iyyar APC ba saboda ta sani za a maimaita abin da ya faru ne a baya.
Haɗakar Kwankwaso, Obi ta fara karfi
Kun ji cewa tsohon gwamnan Kano, Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi magana kan yiwuwar yin haɗaka da dan takarar shugaban kasa a LP, Peter Obi.
Haka zalika jam'iyar LP ta yi martani da ke nuna amincewa da hadakar bayan maganar da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng