'Mene Dalilin Kiran Sunana Kadai', Gwamna Ya Kalubalanci Tinubu kan Rigimar Ribas

'Mene Dalilin Kiran Sunana Kadai', Gwamna Ya Kalubalanci Tinubu kan Rigimar Ribas

  • Gwamna Siminalayi Fubara ya nuna damuwa kan matsayar da Bola Tinubu ya dauka game da rikicin Rivers
  • Sumi Fubara ya ce bai ji dadin yadda Tinubu ya kira sunansa shi kadai ba bayan kowa ya san inda matsalar take
  • Hakan ya biyo bayan samun rigimar da ya yi sanadin rasa rayuka da kona dukiyoyi bayan zaben kananan hukumomi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Gwamna Siminalayi Fubara ya yi magana kan rikicinsa da tsohon gwamnan Rivers, Nyesom Wike.

Mai girma Simi Fubara ya nuna damuwa kan yadda Bola Tinubu ya kira sunansa shi kadai yayin maganarsa a kan rikicin.

Gwamna ya kalubalanci Tinubu bayan ya yi martani kan rigimar siyasa
Gwamna Siminalayi Fubara bai ji dadin yadda Bola Tinubu ya kira sunansa shi kadai ba a rigimar Rivers. Hoto: @DOlusegun, Sir Siminalayi Fubara.
Asali: Twitter

Bola Tinubu ya magantu kan rigimar jihar Rivers

Kara karanta wannan

"Ba komai za ka yi nasara ba": Gwamna ga minista, ya fadi silar rikici tsakaninsu

Gwamnan ya bayyana haka ne a cikin faifan bidiyon YouTube da Channels TV ta wallafa a daren jiya Litinin 7 ga watan Oktoban 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan ya biyo bayan martanin Tinubu kan rigimar da ta ki karewa inda ya ba Gwamna Fubara shawara.

Tinubu ya bukaci Fubara da sauran yan siyasa da masu ruwa da tsaki a jihar su nuna juriya da kuma bin doka da oda.

Gwamna Fubara bai ji dadin kalaman Tinubu ba

Fubara ya ce ba shi da matsala da tsoma baki da Tinubu ya yi amma ya ce kowa ya san inda matsalar take.

Ya ce ba shi ne babbar matsala ba a rikici tsakaninsa da tsohon mai gidansa, Nyesom Wike.

"Ba ni da wata matsala da tsoma baki da Tinubu ya yi, damuwa ta shi ne yadda ya kira sunana ni kadai."

Kara karanta wannan

Tinubu ya yi magana kan kone kone a Rivers, ya ba yan sanda zazzafan umarni

"Wannan abu ne mai sauki, kowa a jihar Rivers ya san daga inda matsalar take, ba Fubara ne matsala ba."

- Siminalayi Fubara

Fubara ya fadi musabbabin kara rikicewar matsalar a jihar bayan kammala zaben kananan hukumomi da aka yi a jihar.

Gwamna Fubara ya shawarci Wike kan rigimar Rivers

Kun ji cewa Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya roki Ministan Abuja, Nyesom Wike da ya bar rigimar jihar ta wuce.

Gwamnan ya ce bai kamata tsohon gwamnan ya ce sai ya yi nasara kan dukan fadan da ya ke yi ba musamman a jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.