Ana Fargabar Jami'an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Kada Kuri'a, Sun Kwace Kayan Zaben

Ana Fargabar Jami'an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Kada Kuri'a, Sun Kwace Kayan Zaben

  • Ana zargin jami'an tsaro da kansu sun kai farmaki kan masu zabe inda suka watsa su a jihar Rivers
  • An tabbatar da cewa jami'an tsaron sun shiga harabar makarantar firamare ta Elakahia da tarwatsa masu zabe
  • Hakan na zuwa ne yayin da ake gudanar da zaben ƙananan hukumomi a yau Asabar 5 ga watan Oktoban 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Rivers - Ana fargabar jami'an tsaro sun tarwatsa masu gudanar da zabe a jihar Rivers.

Lamarin ya faru ne a yau Asabar 5 ga watan Oktoban 2024 a makarantar firamare ta Elakahia da ke Port Harcourt.

Ana zargin jami'an tsaro da wargaza masu zaɓe a jihar Rivers
Zaben kananan hukumomi a jihar Rivers ya dawo rigima a wurare da dama. Hoto: Nigeria Police Force, Sir Siminalayi Fubara.
Asali: Facebook

Rivers: Ana zargin jami'an tsaro sun tarwatsa zaɓe

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun fatattaki masu sallar juma'a a wasu masallatai a Katsina

Channel TV ta wallafa wani bidiyo inda aka gano yadda wasu cikin kayan jami'an tsaro suka watsa masu zaɓen.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Masu zaben da ke zargin wadanda suka watsa taron jami'an tsaro ne sun koka kan yadda aka watsa masu barkonon tsohuwa.

Jami'an da ke gudanar da zaben daga hukumar INEC sun gama shiri domin fara zaben kafin aka watsa su.

An tarwatsa masu zaɓe da kwace kayansu

Jami'an tsaron da ake zargin sun shigo farfajiyar makarantar ne rike da makamai inda suka kori dukan mutane da ke ciki waje.

Daga bisani, an tabbatar da cewa jami'an tsaro sun kwashe kayayyakin zaben da aka fama shirya su a wurin.

Daya daga cikin jami'an ya ci zarafin wani ma'aikacin wucin gadi na INEC inda ya ce masa ya cire rigar aikin da ke jikinsa.

Kara karanta wannan

Gwamna ya ja daga, ya ce zai iya rasa ransa saboda adalci a zaben gobe

"Zo nan wurin, ka cire wannan riga da ka saka ta INEC, mene ka ke yi a nan?"

- Cewar wata majiya

Zanga-zanga ta barke ana gudanar da zabe

Kun ji cewa magoya bayan ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike sun fito kan tituna domin nuna adawarsu da zaɓen ƙananan hukumomin da ake yi a jihar Rivers.

Masu zanga-zangar sun buƙaci Gwamna Siminalayi Fubara da ya bi umarnin kotu wanda ya hana a gudanar da zaɓen a jihar.

Zanga-zangar na zuwa ne yayin da mutane suka fito domin kaɗa ƙuri'unsu a zaɓen na ranar Asabar mai cike da cece-kuce.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.