"Har Yanzu a Firgice Ka Ke": Doguwa Ya Mayarwa Kwankwaso Martani kan Kalamansa

"Har Yanzu a Firgice Ka Ke": Doguwa Ya Mayarwa Kwankwaso Martani kan Kalamansa

  • Dan Majalisar Tarayya da ke wakiltar Tudun Wada/Doguwa a Kano ya mayarwa Rabiu Kwankwaso martani
  • Hon. Alhassan Ado Doguwa ya ce har yanzu Kwankwaso a kidime yake bayan faduwa zaben 2023 a hannun Tinubu
  • Doguwa ya shawarci Kwankwaso ya mayar da hankali kan zaben 2027 inda za a yi masa ritaya gaba daya a siyasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Dan Majalisar Tarayya a jihar Kano, Alhassan Ado Doguwa ya soki Sanata Rabiu Kwankwaso.

Doguwa ya mayar da martani kan kalaman Kwankwaso inda ya ke sukar gwamnatin Bola Tinubu.

Doguwa ya mayar da martani ga Kwankwaso kan kalamansa
Hon. Alhassan Ado Doguwa ya yi martani ga kalaman Rabi'u Musa Kwankwaso. Hoto: Rabi'u Musa Kwankwaso, Hon. Alhassan Ado Doguwa TV.
Asali: Facebook

2027: Ado Doguwa ya caccaki Kwankwaso

Dan Majalisar ya bayyana haka ne ga manema labarai a Kano a yau Juma'a 4 ga watan Oktoban 2024, cewar Tribune.

Kara karanta wannan

'Ya lalata komai,' Kwankwaso ya tono 'barnar' da Ganduje ya yi a Kano

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Doguwa ya ce har yanzu Kwankwaso bai gama warkewa daga faduwar zaben da ya yi a 2023 ba.

Hon. Doguwa ya ce Kwankwaso ba shi da mutuncin da zai yi magana a madadin yan Arewa gaba daya.

"Tsohon gwamnan Kano har yanzu bai gama warwarewa ba bayan faduwa zaɓe a hannun Bola Tinubu a 2023."
"Shiyasa tun yanzu ya rikice inda ya ke babatu kan zaben 2027 mai zuwa."

- Alhassan Ado Doguwa

Ado Doguwa ya ba Kwankwaso shawara

Hon. Doguwa ya shawarci Kwankwaso ya mayar da hankali a 2027 da za a yi masa ritaya daga siyasa, The Guardian ta ruwaito.

Ya ce Bola Tinubu yana kokarin samar da abubuwan more rayuwa ga yan kasa saboda haka babu buƙatar dauke masa hankali.

Wannan na zuwa ne bayan Rabiu Kwankwaso ya bayyana cewa yan Najeriya musamman yan Arewa sun gaji da mulkin Tinubu.

Kara karanta wannan

'Yan APC maƙiya talaka ne,' Kwankwaso ya kawo mafita da ya illata jam'iyyar

Kwankwaso ya fadi haka ne a jiya Alhamis 3 ga watan Oktoban 2024 inda ya ce yan kasar sun zaku a sake zaben domin kawar da Tinubu.

Kwankwaso ya magantu kan zama mataimakin Obi

A wani labarin, kun ji cewa Sanata Rabiu Kwankwaso ya yi magana kan yiwuwar zama mataimakin Peter Obi a zaben 2027.

Kwankwaso ya ce shi ba sa'an Obi ba ne a siyasa da kuma ilimi sai dai ya ce hakan ba matsala ba ne a wurinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.