Gwamna Ya Bayar da Hutu a Ranakun Alhamis da Juma'a a Jiharsa, Bayanai Sun Fito

Gwamna Ya Bayar da Hutu a Ranakun Alhamis da Juma'a a Jiharsa, Bayanai Sun Fito

  • Gwamnan jihar Ribas ya ayyana Alhamis da Jumu'a a matsayin ranakun hutu domin ba ma'aikata damar komawa yankunansu
  • Siminalayi Fubara ya ce ya ɗauki wannan matakin ne domin mutane su koma gida su kaɗa kuri'unsu a zaɓen kananan hukumomi ranar Asabar
  • Ya kuma sanar da taƙaita zirga-zirgar ababen hawa daga tsakar daren ranar Juma'a zuwa ƙarfe 5:00 na yammacin Asabar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rivers - Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas ya ayyana ranakun Alhamis da Juma'a, 3 da 4 ga watan Oktoba, 2024 a matsayin ranakun hutu.

Gwamna Fubara ya ba da hutun kwanaki biyun ne domin bai wa ma'aikata damar komawa yankunansu domin kaɗa kuri'a a zaɓen kananan hukumomin da za a yi.

Kara karanta wannan

Nasarawa: NASIEC ta shirya gudanar da zaben ciyamomi, an fitar da jadawali

Gwamna Fubara na Ribas.
Gwamna Fubara ya ba da hutun kwanaki 2 saboda zaben kananan hukumomi a Ribas Hoto: Sir Siminalayi Fubara
Asali: Facebook

Daily Trust ta ruwaito cewa hukumar zaɓen jihar Ribar ta shirya gudanar da zaɓen kananan hukumomi ranar Asabar mai zuwa, 5 ga watan Oktoba, 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna ya taƙaita zirga-zirga a Ribas

Gwamnan ya kuma sanar da takaita zirga-zirgar ababen hawa daga tsakar daren ranar Juma’a, 4 ga watan Oktoba zuwa karfe 5:00 na yamma a ranar zaben.

Siminalayi Fubara ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya yi kai tsaye ga mazauna Ribas daga gidan gwamnati da ke Fatakwal ranar Laraba.

Ya ce za a yi zaɓen ne bayan ƙarewar wa'adin ciyamomi da kansiloli a faɗin kananan hukumomi 23 ranar 17 ga watan Yuni, 2024, rahoton Channels tv.

Dalilin shirya zaɓen ƙananan hukumomi

A cewarsa, tun bayan karewar wa'adin ciyamomin, ya naɗa kantomomin da za su kula da harkokin kananan hukumomin gabanin hukumar RSIEC ta shirya zaɓe.

Kara karanta wannan

1 ga Oktoba: Kotu ta yanke hukunci kan zanga zangar da ake shirin yi, ta jero wurare 4

Fubara ya ce hakan ya biyo bayan hukuncin kotun ƙoli na bai wa kananann hukumomi cikakkiyar damar cin gashin kai tare da umarnin daina tura kason waɗanda ba su da zaɓaɓɓun ciyamomi.

Gwamnan ya ce bayan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sa baki, an tsawaita wa'adin fara aikin dojar da watanni uku wanda zai kare ranar 31 ga watan Oktoba.

"Saboda haka mun ba da hutun ranakun Alhamis da Juma'a, 3 da 4 ga watan Oktoba, 2024 don mutane su koma yankunansu su kaɗa kuri'a,' in ji Fubara.

Gwamna Fintiri ya roki Wike da Fubara

A wani labarin kuma gwamnan Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri ya yi magana kan rikicin siyasar jihar Rivers.

Gwamna Fintiri ya roƙi ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike da gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara da su kawo ƙarshen rikicin siyasar jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262